Zanga Zanga: NYSC Ta Soke CDS a Watan Agusta, Ta Aika Sako ga ’Yan Bautar Kasa

Zanga Zanga: NYSC Ta Soke CDS a Watan Agusta, Ta Aika Sako ga ’Yan Bautar Kasa

  • Hukumar NYSC ta sanar da dakatar da dukkanin wasu ayyuka na masu yiwa kasa hidima na watan Agusta a fadin kasar nan
  • An dage shirin tantancewa da hidimtawa al’umma na wata-wata (CDS) ga mambobin NYSC saboda zanga-zangar da ake shirin yi
  • Hukumar NYSC ta bayyana cewa za a sanar da ranar da 'yan bautar kasar za su ci gaba da yin shirin CDS din nan gaba kadan

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Hukumar NYSC ta dage shirin tantancewa da yiwa al'umma hidima na wata-wata (CDS) ga 'yan bautar kasa saboda shirin gudanar da zanga-zanga a fadin kasar.

A ranar 1 zuwa 10 ga watan Agusta ne matasa suka shirya gudanar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da kuma matsalar tattalin arziki.

Kara karanta wannan

'Yan siyasa da kungiyoyi da ke goyon bayan zanga zanga da wadanda suka kushe tsarin

NYSC ta fadi matakin da ta dauka yayin da matasa ke shirin yin zanga-zanga
Hukumar NYSC ta ce za ta sanar da ranar da za ci gaba da shirin CDS. Hoto: @officialnyscng
Asali: Twitter

NYSC ta aika sako ga 'yan bautar kasa

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takarda da aka aika zuwa ga shugabannin NYSC na jihohi, jami'an kananan hukumomi (LGIs), da jami'an shiyya (ZI), inji rahoton The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Takardar ta bayyana cewa NYSC ba ta lamuncewa masu yi wa kasa hidima shiga zanga-zangar da ka iya haifar da tabarbarewar doka da oda a kasar ba.

"Ana sanar da dukkanin masu yi wa kasa hidima cewa an dakatar da tantancewa da ayyukan CDS na wata-wata har sai an fitar da sanarwar dawowar shirin."

Zanga-zanga: NYSC ta gargadi matasa

A baya Legit Hausa ta rahoto cewa hukumar NYSC ta gargadi ‘yan bautar kasa kan shiga zanga-zangar da aka shirya yi a fadin kasar a ranakun 1 zuwa 10 ga watan Agusta.

Kara karanta wannan

NSDC ta bankado shirin 'yan ta'adda a lokacin zanga-zanga, ta fadi matakin da ta dauka

Yetunde Baderinwa, kodinetan hukumar na jihar Legas, ya ce duk wani dan bautar kasa da aka kama yana gudanar da zanga-zanga, za a hukunta shi kamar yadda dokar NYSC ta gindaya.

A cewar Baderinwa, shirin na NYSC an yi shi ne domin hada kan ‘yan Najeriya kuma 'yan bautar da ke shiga zanga-zangar za su yi hannun riga da manufar hukumar ta NYSC.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.