Matakan Gaggawa 10 da Gwamnatin Tinubu Ta Dauka Daga Jin Za a Shirya Zanga Zanga

Matakan Gaggawa 10 da Gwamnatin Tinubu Ta Dauka Daga Jin Za a Shirya Zanga Zanga

Abuja - Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yi duk abubuwan da za ta iya domin ganin ta hana a shiga zanga-zangar lumuna a Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Gwamnatin tarayya ta bi hanyoyi iri-iri da kuma wasu dabaru da matakai da ake ganin an nufe su ne domin shawo kan matasan kasar.

Legit Hausa ta jero wadannan matakai da tsare-tsare da aka fito da su a gurguje:

Bola Tinubu
Bola Tinubu bai so a shiga zanga zanga a Najeriya Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

1. Karin albashin ma’aikata

Duk da an yi watanni ana tattaunawa, gwamnatin tarayya ta yi maza ta kara mafi karancin albashi daga N38, 000 zuwa N70, 000 a Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kafin a ce kobo, shugaban kasa ya tsaida magana kuma ya kai kudiri gaban ‘yan majalisa, su ma ba su bata lokaci ba suka amince da batun.

Kara karanta wannan

Kungiyar TUC ta tsame kanta daga zanga zanga, ta turawa jami'an tsaro sako

2. Tinubu ya zauna da ‘yan kwadago

Shugaba Bola Tinubu ya yi kokarin zama da ‘yan kwadago domin su amince da karin, kuma ya yi masu wasu alkawura ya shawo kan su.

Wannan ya taimaka wajen hana ‘yan kwadago ba zanga-zangar karfi, wanda hakan ya na iya kai wa ga yin yajin-aiki da zai mamaye kasar.

3. Zanga-zanga: Taron Shugaban kasa da malamai

An rahoto yadda gwamnatin tarayya ta yi zama da malaman addini da nufin a hana matasa hawa tituna da sunan zanga-zangar lumana.

Malamai sun yi ta kokarin yin wa’azi a mimbari domin fadakar da matasa da gwamnati.

4. Tinubu ya hadu da Sarakuna kan zanga-zanga

Shugaban kasa ya sa an kira masa sarakunan gargajiya inda ya lallabe su kan batun. George Akume ya wakilce shi a zaman da aka shirya.

5. Rabon kudi da tallafi

A ‘yan kwanakin nan aka aji gwamnatin tarayya ta fara rabon shinkafa. Tuni dai tireloli sun isa wasu jihohi da nufin rage yunwar da ake yi.

Kara karanta wannan

"Ban da lalata kadarori": Tinubu ya fadi yadda ya shiga zanga zanga a lokacin soja

Premium Times ta ce gwamnati ta fitar da sama da N438bn a rabawa Abuja da jihohi 34 a karkashin NG-CARES domin rage talauci.

6. Ministocin Tinubu sun tashi tsaye

Ministoci su na ta kokari wajen gamsar da al’umma cewa an fito da tsare-tsare da za su magance matsin rayuwa da kuncin da ake ciki a yau.

7. Tallafin kudi ga matasa

Ana haka ne kuma aka ji Ministar cigaban matasa, Dr. Jamila Ibrahim Bio ta ce kwanan nan za a fito da tsarin rabon tallafin N110bn ga matasa.

Jamila Bio ta ce an fito da shirin YIF ne da nufin tallafawa matasa da jarin Naira biliyan 100 domin inganta sana'o'i da kuma tattalin arziki.

8. Gwamnatin tarayya ta raba jari

A jihar Jigawa, an ji yadda gwamnatin Tinubu ta raba N50, 000 ga kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa a karkashin jagorancin Kashim Shettima.

9. Lamunin karatu zai hana zanga-zanga?

Kara karanta wannan

Gwamnoni da wasu ministoci sun fara koƙarin hana matasa zanga zangar da suke shirin yi

Maganar lamunin karatu yana neman ya tabbata bayan an dade ana je-ka-ka-dawo, ana tunanin hakan zai iya kwantar da hankalin dalibai.

10. Sadaukar da rabin albashin ‘yan majalisa

Su kuwa ‘yan majalisar wakilan tarayya sun sadaukar da rabin albashin da ake biyansu a wata duk saboda ganin an biyawa jama’a bukatunsu.

‘Yan majalisar sun ba da shawarar a zauna da matasa domin a hana su hawa tituna.

An nemi a hakura da zanga-zanga

Rahoton nan ya nuna cewa Kashim Shettima ya ba ƴan Najeriya shawarar su yi watsi da maganar shirya zanga-zangar lumana a Najeriya.

Mataimakin shugaban ƙasan ya buƙaci a haƙura da fitowa kan tituna yin zanga-zanga, ya nuna cewa yanzu ba lokacin yin hakan ba ne ko kaɗan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng