An Gano Jihohin da Mamakon Ruwa Zai Jawo Gagarumar Ambaliya

An Gano Jihohin da Mamakon Ruwa Zai Jawo Gagarumar Ambaliya

  • Gwamnatin tarayya ta yi gargadin za a yi ambaliyar ruwa a garuruwan kasar nan 94 cikin kwanaki biyar
  • Ministan muhalli, Dr. Iziak Salako ya ce ambaliyar za ta afku a jihohi 22 daga cikin 36 da ake da su a Najeriya
  • Dakta Salako ya ce daga cikin jihohi akwai Adamawa, Kano, Jigawa, Yobe, Katsina da Kebbi

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta yi gargadin samun gagarumar ambaliya a jihohin kasar nan 22.

Garuruwa 94 ne ake fargabar ruwa zai shanye saboda mamakon ruwa da za a yi na kwanaki biyar- daga ranar Talata 16 Yuli, 2024 zuwa 20 Yuli, 2024.

Kara karanta wannan

Takun saƙar Wike da Fubara: Jigon PDP ya faɗi hanyoyi 4 na magance rikicin Rivers

Ambaliya
Gwamnati ta yi hasashen ambaliya a jihohi 22 Hoto: Pius Utomi Ekpei/ Sodiq Adelakun
Asali: Getty Images

A wani rahoto da ya kebanta da Jaridar Punch, Ministan muhalli, Dr. Iziak Salako ya ce akwai fargabar ruwan zai yi barna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jihohi da yankunan da za ayi ambaliya

Minista Iziak Salako ya ce ruwa kamar da bakin kwarya zai shafi wasu yankuna a jihohi da ke Arewa da Kudancin Najeriya.

Jihohin da yankunan da ake hasashen ambaliya za ta shafa sun hada da;

1. Adamawa - Gbajili, Ganye

2. Abia - Eziama, Arochukwu

3. Anambra - Onitsha

4. Akwa Ibom - Uyo, Upenekang, Oron, Edor, Eket, Obianga, Etinan 5. Bauchi -Tafawa Balewa, Bauchi

6. Bayelsa - Letugbene

7. Borno State Maiduguri

8. Cross River Ikom, Calabar, Itigidi, Akpap

9. Nasarawa - Udeni, Tunga

10. FCT - Abaji, Bwari 11. Jigawa - Miga, Ringim, Dutse, Hadejia

Kara karanta wannan

Riga malam masallaci: An hango allon kamfen Bola Tinubu na zaben 2027

12. Kano - Gezawa, Gwarzo, Kano, Karaye, Wudil, Sumaila

13. Kebbi - Gwandu, Jega, Kangiwa, Gauri-Banza, Ribah, Sakaba, Saminaka, Kamba, Birnin Kebbi, Bunza, Argungu, Bagudo 14.Katsina - Bindawa, Jibia, Kaita, Katsina, Daura, Funtua 15. Kwara - Kosubosu)

16. Niger - Ibi, Bida, Kontagora, Mashegu, Minna, New Bussa, Katcha, Rijau, Wushishi 17. Plateau -Jos, Mangu

18. Rivers - Port-Harcourt, Onne, Okrika, Bori

19. Sokoto - Makira, Goronyo, Isa, Silame, Sokoto, Wamako 20. Taraba - Gembu, Beli, Garkowa, Gasol, Serti, Donga, Duchi, Gwarzo, Gun gun Bodel

21. Yobe -Gashua, Gasma, Damaturu, Geidam, Kanama

22. Zamfara - Kaura Namoda, Maradun, Shinkafi, Bukkuyum, Majara, Gummi

Ruwa ya yi barna a Yobe

A baya mun ruwaito cewa mamakon ruwan sama a jihar Yobe ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane uku a karamar hukumar Nangere.

Shugaban hukumar bayar da agaji na jihar, Dakta Muhammad Goje da ya tabbatar da lamarin, ya ce ruwan ya lalata gidaje 50.

Kara karanta wannan

Bashin Naira tiriliyan 37: Gwamnan CBN ya fadi ainihin abin da ya jawo tsadar abinci

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.