An Gano Jihohin da Mamakon Ruwa Zai Jawo Gagarumar Ambaliya

An Gano Jihohin da Mamakon Ruwa Zai Jawo Gagarumar Ambaliya

  • Gwamnatin tarayya ta yi gargadin za a yi ambaliyar ruwa a garuruwan kasar nan 94 cikin kwanaki biyar
  • Ministan muhalli, Dr. Iziak Salako ya ce ambaliyar za ta afku a jihohi 22 daga cikin 36 da ake da su a Najeriya
  • Dakta Salako ya ce daga cikin jihohi akwai Adamawa, Kano, Jigawa, Yobe, Katsina da Kebbi

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta yi gargadin samun gagarumar ambaliya a jihohin kasar nan 22.

Garuruwa 94 ne ake fargabar ruwa zai shanye saboda mamakon ruwa da za a yi na kwanaki biyar- daga ranar Talata 16 Yuli, 2024 zuwa 20 Yuli, 2024.

Kara karanta wannan

Takun saƙar Wike da Fubara: Jigon PDP ya faɗi hanyoyi 4 na magance rikicin Rivers

Ambaliya
Gwamnati ta yi hasashen ambaliya a jihohi 22 Hoto: Pius Utomi Ekpei/ Sodiq Adelakun
Source: Getty Images

A wani rahoto da ya kebanta da Jaridar Punch, Ministan muhalli, Dr. Iziak Salako ya ce akwai fargabar ruwan zai yi barna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jihohi da yankunan da za ayi ambaliya

Minista Iziak Salako ya ce ruwa kamar da bakin kwarya zai shafi wasu yankuna a jihohi da ke Arewa da Kudancin Najeriya.

Jihohin da yankunan da ake hasashen ambaliya za ta shafa sun hada da;

1. Adamawa - Gbajili, Ganye

2. Abia - Eziama, Arochukwu

3. Anambra - Onitsha

4. Akwa Ibom - Uyo, Upenekang, Oron, Edor, Eket, Obianga, Etinan 5. Bauchi -Tafawa Balewa, Bauchi

6. Bayelsa - Letugbene

7. Borno State Maiduguri

8. Cross River Ikom, Calabar, Itigidi, Akpap

9. Nasarawa - Udeni, Tunga

10. FCT - Abaji, Bwari 11. Jigawa - Miga, Ringim, Dutse, Hadejia

Kara karanta wannan

Riga malam masallaci: An hango allon kamfen Bola Tinubu na zaben 2027

12. Kano - Gezawa, Gwarzo, Kano, Karaye, Wudil, Sumaila

13. Kebbi - Gwandu, Jega, Kangiwa, Gauri-Banza, Ribah, Sakaba, Saminaka, Kamba, Birnin Kebbi, Bunza, Argungu, Bagudo 14.Katsina - Bindawa, Jibia, Kaita, Katsina, Daura, Funtua 15. Kwara - Kosubosu)

16. Niger - Ibi, Bida, Kontagora, Mashegu, Minna, New Bussa, Katcha, Rijau, Wushishi 17. Plateau -Jos, Mangu

18. Rivers - Port-Harcourt, Onne, Okrika, Bori

19. Sokoto - Makira, Goronyo, Isa, Silame, Sokoto, Wamako 20. Taraba - Gembu, Beli, Garkowa, Gasol, Serti, Donga, Duchi, Gwarzo, Gun gun Bodel

21. Yobe -Gashua, Gasma, Damaturu, Geidam, Kanama

22. Zamfara - Kaura Namoda, Maradun, Shinkafi, Bukkuyum, Majara, Gummi

Ruwa ya yi barna a Yobe

A baya mun ruwaito cewa mamakon ruwan sama a jihar Yobe ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane uku a karamar hukumar Nangere.

Shugaban hukumar bayar da agaji na jihar, Dakta Muhammad Goje da ya tabbatar da lamarin, ya ce ruwan ya lalata gidaje 50.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Kara karanta wannan

Bashin Naira tiriliyan 37: Gwamnan CBN ya fadi ainihin abin da ya jawo tsadar abinci

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng