Kano: Masallata Sun Rasa Ransu Bayan Tirela Ta Bi Kansu Ana Tsaka da Jam'in Juma'a

Kano: Masallata Sun Rasa Ransu Bayan Tirela Ta Bi Kansu Ana Tsaka da Jam'in Juma'a

  • An shiga wani irin yanayi bayan wasu masallata sun rasa ransu suna tsaka da sallah a masallacin Juma'a bayan tirela ta hau kansu
  • Lamarin ya faru ne a garin Imawa da ke karamar hukumar Kura a jihar Kano a yau Juma'a 28 ga watan Yunin 2024
  • Hukumar kiyaye hadura ta kasa, FRSC ita ta tabbatar da haka inda ta ce akalla mutane 14 sun mutu sanadin hatsarin motar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Hukumar kiyaye haduara ta kasa, FRSC ta tabbatar da mutuwar masallata akalla 14 a jihar Kano.

Hukumar ta tabbatar da cewa masallatan sun rasa ransu bayan tirela ta kutsa cikin jam'i a masallacin Juma'a.

Kara karanta wannan

Za a sha jar miya: Tinubu zai fara biyan tallafin N150bn ga 'yan kasa, jama'a za su caba

Wasu masallata 14 sun rasu bayan tirela ta bi kansu a Kano
Babbar mota ta hallaka wasu masallata 14 yayin sallar Juma'a a Kano.
Asali: Original

A ina iftila'in ya faru a Kano?

Lamarin ya faru ne a garin Imawa da ke karamar hukumar Kura kan hanyar Kano zuwa Kaduna da misalin karfe 1:30 na rana, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

FRSC ta tabbatar da cewa direban ya gagara shawo kan motar inda ya kutsa kan jama'a a yau Juma'a 28 ga watan Yunin 2024.

Kakakin rundunar reshen jihar Kano, Abdullahi Labaran ya ce an binne tara daga cikin wadanda suka rasu a yau Juma'a da rana, Punch ta tattaro.

Kano: Ana ci gaba da basu kulawa

Labaran ya ce sauran wadanda suka samu raunuka kuma suna ci gaba da karbar kulawa a asibiti.

Ya kara da cewa yanzu haka direban ya gudu ba a san ina yake ba inda ya tura sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasu.

Kara karanta wannan

Yayin da ake rade radin tuge shi, Sultan ya tura sako ga rundunar sojoji

An samu karin mamata a harin masallaci

Kun ji cewa an samu ƙarin mutanen da suka rasu sakamakon harin da wani matashi ya kai Masallaci a Larabar Abasawa, karamar hukumar Gezawa a Kano.

Shafi’u Abubakar, ɗan kimanin shekaru 38 ne ya bankawa Masallacin wuta yayin da mutane ke tsaka da Sallar Asubah a watan Mayun da ya gabata.

Rahotanni sun tabbatar da cewa adadin waɗanda suka rasu sakamakon kona masallata a masallacin da wani matashi ya yi sun ƙaru zuwa 23

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel