Tinubu Ya Amince da Ba Gidaje Miliyan 3 Tallafin N50,000, an Fayyace Tsarin Shirin

Tinubu Ya Amince da Ba Gidaje Miliyan 3 Tallafin N50,000, an Fayyace Tsarin Shirin

  • Yayin da ake cikin mawuyacin hali a Najeriya, Shugaba Bola Tinubu ya amince da kawo sauki ga iyalai miliyan uku a kasar
  • Tinubu ya amince da ba da N50,000 ga iyalai a duka shiyyoyin kasar har na tsawon watanni uku domin rage musu radadi
  • Wannan na zuwa ne bayan ganawa na musamman da gwamnonin kasar baki daya a yau Alhamis 27 ga watan Yunin 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shugaban kasa, Bola Tinubu ya amince da raba N50,000 ga iyalan Najeriya har miliyan 3.6.

Tallafin zai zo ne karkashin hukumar tallafawa iyalai domin rage musu radadin halin da ake ciki yanzu a kasar.

Kara karanta wannan

Bukatar Bola Tinubu ta jawo zazzafar muhawara a Majalisar Tarayya, hayaniya ta ɓarke

Tinubu zai gwangwaje iyalai a Najeriya da tallafin N50,000
Bola Tinubu zai ba iyalai 3.6m da tallafin N50,000 a fadin Najeriya. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Tinubu zai tallafawa Iyalai N50,000-N100,000

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadimin Tinubu a bangaren yada labarai, Ajuri Ngelale ya fitar a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tallafin zai kunshi akalla iyalai 50,000 zuwa 100,000 daga duka jihohin Najeriya har na tsawon watanni uku.

Yadda tsarin tallafin Tinubu zai kasance

"Shugaba Tinubu ya amince da raba tallafi ga iyalai a duka shiyyoyi guda shida da ke Najeriya karkashin hukumar tallafawa iyalai."
"Daga cikin abubuwan da ke karkashin shirin akwai siyan motoci masu amfani da gas da bas bas domin inganta al'umma."
"Za a ba da tallafin 50,000 ga iyalai akalla 100,000 a kowace jiha da ke Najeriya har na tsawon watanni uku."

Ajuri Ngelale

Wannan na zuwa ne yayin da 'yan kasar ke cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa da kuma hauhawan farashin kaya.

Kara karanta wannan

Yayin da ake rade radin tuge shi, Sultan ya tura sako ga rundunar sojoji

Tinubu zai ba da tallafin N50,000

A wani labarin mai kama da wannan, mun kawo muku cewa Gwamnatin Tarayya ta fitar da sabuwar sanarwa kan ba 'yan Najeriya tallafin N50,000.

Wannan tallafi na daga cikin tsarin shugaban kasa Tinubu na ba da tallafin rage radadi (PCGS) domin kawowa jama'a saukin rayuwa.

Za a bada tallafin ne ga kananan 'yan kasuwa da kuma masu sana'o'i a fadin kasar domin rage radadin halin da ake ciki a yanzu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel