Bola Tinubu Yana Jagorantar Taron FEC a Fadar Shugaban Kasa, Bayanai Sun Fito

Bola Tinubu Yana Jagorantar Taron FEC a Fadar Shugaban Kasa, Bayanai Sun Fito

  • Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci taron majalisar zartarwa (FEC) a fadar gwamnatinsa da ke birnin tarayya Abuja
  • Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume da shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila sun halarci taron
  • Wannan zama na zuwa ne mako shida bayan taron yini biyu da FEC ta yi a watan jiya, wanda aka amince da tsare-tsare da ayyuka 20

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Bola Ahmed Tinubu na jagorantar taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) yanzu haka a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Taron na gudana ne a ɗakin taron majalisar da ke fadar gwamnatin Najeriya yau Talata, 25 ga watan Yuni, 2024.

Kara karanta wannan

Bola Tinubu ya ɗauki mataki kan sabon mafi ƙarancin albashi a taron majalisar zartarwa

Taron FEC karkashin Tinubu.
Bola Ahmed Tinubu ya shiga taron majalisar zartarwa a Abuja Hoto: @NGRPresident
Asali: Twitter

Majalisar FEC ta zauna bayan makonni

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, taron FEC na yau na zuwa ne bayan wanda aka yi kwana biyu ana yi kusan makonni shida da suka gabata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A zaman FEC na ƙarshe. gwamnatin Bola Tinubu ta amince da ayyuka daban-daban har guda 20.

Galibin ministoci sun halarci taron FEC

Waɗanda suka halarci taron da ke gudana yanzu haka sun haɗa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da shugaban ma'aikatan fadar gwamnati Femi Gbajabiamila.

Bugu da ƙari, an tattaro cewa mafi akasarin ministocin Bola Tinubu sun halarci taron majalisar a wannan karon, rahoton Leadership.

Canza ranar zaman majalisar FEC

Idan za ku iya tunawa Shugaba Tinubu ya kaddamar da majalisar ne ranar 28 ga watan Augusta, 2023 kuma ya sauya ranakun taron daga Laraba zuwa Litinin a kowane mako.

Kara karanta wannan

Tinubu ya sake ɗauko tsohon kwamishinansa, ya naɗa shi a shirgegen muƙami

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, a ranar 16 ga Oktoba, 2023, ya bayyana cewa majalisar za ta rika zama ne idan akwai muhimman batutuwan da za a duba.

"Saboda haka daga yanzu taron FEC ya koma ranakun Laraba kuma ba lallai ne kowane mako za a yi taron ba, idan babu batun da za a tattauna, za a ɗaga zuwa mako na gaba."

Tinubu ya naɗa shugaban FCCPC

A wani labarin na daban Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Mr. Olatunji Bello a matsayin shugaban hukumar FCCPC ta ƙasa.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya tabbatar da wannan naɗi a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, 24 ga watan Yuni, 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262