Rigima Ta Kaure Tsakanin ’Yan Bindiga, Su Na Ta Kashe Junansu da Kansu a Jejin Zamfara

Rigima Ta Kaure Tsakanin ’Yan Bindiga, Su Na Ta Kashe Junansu da Kansu a Jejin Zamfara

  • Tawagar 'yan bindiga biyu ma su hamayya da juna sun kaure da faɗa tsakaninsu kan yunkurin kwace ikon wani yankin Zamfara
  • Lamarin ya faru ne a wani jejin karamar hukumar Maru, jihar Zamfara inda ‘yan ta’addan suka yi kaurin suna wajen farmakar jama'a
  • Majiyoyin leken asiri sun shaida cewa akalla ‘yan ta’adda 16 suka mutu a arangamar, ciki har da wasu manyan jagorori guda biyu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Maru, jihar Zamfara - A wani lamari mai ban mamaki, wasu gungun 'yan bindiga sun kashe junansu a wani kazamin fada da ya kaure tsakanin bangarorin da ke gaba da juna.

Lamarin ya faru ne a wani jejin karamar hukumar Maru, jihar Zamfara inda ‘yan ta’addan suka yi kaurin suna wajen hana jama'a zaman lafiya.

Kara karanta wannan

Sojoji sun cafke masu garkuwa da mutane da suka addabi Taraba, sun ba da bayanai

Fada ya kaure tsakanin kungiyoyin ’yan Bindiga a Zamfara
'Yan bindiga 16 sun mutu yayin da fada ya kaure tsakanin kungiyoyin 'yan ta'addan a Zamfara. Hoto: Legit.ng
Asali: Original

A cewar rahoton da Zagazola Makama ya wallafa a shafinsa na X, fadan ya barke ne a lokacin da wani bangare ya yi yunkurin kwace wani yanki da ke hannun dayan bangaren.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan bindiga 16 sun mutu yayin artabu

An gwabza kazamin fada, inda majiyoyin leken asiri suka shaidawa Zagazola Makama cewa an kashe ‘yan ta’adda akalla 16 a arangamar.

Daga cikin manyan kwamandojin ‘yan fashi da aka halaka a wannan fadan, akwai Alhaji Nagala da Maikube, wadanda suka yi kaurin suna a ta'addanci.

Majiyoyin sun ce an shafe watanni ana takun saka tsakanin bangarorin da ke gaba da juna, inda a makwannin baya-bayan nan rikici ya yi tsamari.

Hukumomi sun yi maraba da fadan

Ana dai kallon wannan arangama a matsayin wani gagarumin koma baya ga kungiyoyin ta'addancin, wadanda suka samu tarwatse sakamakon rarrabuwar kawuna.

Kara karanta wannan

Hankula sun tashi yayin da wani soja ya hallaka farar hula a Abuja

Hukumomin kasar dai sun yi na'am da wannan labari, inda suka bayyana cewa mutuwar 'yan ta'adda wani ci gaba ne mai kyau a fagen yaki da ta'addanci.

Wannan lamarin dai yana nuni da cewa babu amana tsakanin ‘yan ta’adda, za su iya juya wa juna baya, kuma dama akidarsu ta samo asali ne da tashin hankali da barna.

An kama masu garkuwa da mutane

A wani labarin, mun ruwaito cewa sojojin Najeriya sun samu nasarar kama wasu mutane biyu da ake zargin sun kware wajen yin garkuwa da mutane a yankunan jihar Taraba.

Jami'an soji da ke a bataliya ta 6 ne suka kama mutanen bayan shafe watanni suna bibiyarsu, kuma wadanda ake zargin sun amsa laifin tare da bayar da karin bayanan sirri.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel