Bayan Dikko Radda Ya Buɗe Kofa, Gwamna a Arewa Ya Ba Ma'aikata N10,000 Goron Sallah

Bayan Dikko Radda Ya Buɗe Kofa, Gwamna a Arewa Ya Ba Ma'aikata N10,000 Goron Sallah

  • Yayin da ake shirin gudanar da bukukuwan babbar Sallah, Gwamna Bala Mohammed ya tallafawa ma'aikatan jihar Bauchi
  • Gwamnan ya raba kyautar N10,000 ga dukkan ma'aikatan jihar domin gudanar da bukukuwan salla cikin walwala
  • Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da gwamnan ya fitar da safiyar yau Asabar 15 ga watan Mayu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Bauchi - Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya gwangwaje ma'aikata a jihar da abin alheri.

Bala ya raba kyautar N10,000 ga duka ma'aikatan jihar domin gudanar da bukukuwan sallah cikin walwala.

Gwamna ya gwangwaje ma'aikata da kyautar N10,000 na goron sallah
Gwamna Bala Mohammed ya ba ma'aikata goron sallah N10,000. Hoto: Senator Bala Mohammed.
Asali: UGC

Sallah: Bala Mohammed ya tallafawa ma'aikata

Gwamnan ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook da safiyar yau Asabar 15 ga watan Yuni.

Kara karanta wannan

Sallah: Gwamna Lawal ya kafa tarihi, ma'aikata sun karɓi albashin da ba su taɓa gani ba

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanata Bala ya ce ya yi hakan ne domin ragewa jama'a halin da suke ciki ganin yadda ake fama da tsadar rayuwa.

"Lura da halin ƙunci da tsadar rayuwa da muka tsinci kanmu a ciki a wannan lokaci da muke shirin bikin Sallah, na amince da biyan tallafin dubu goma-goma ga ɗaukacin ma’aikata."
"Na dauki wannan matakin ne domin rage raɗaɗin da mutane ke ciki."

- Bala Mohammed

Gwamnan ya kara da cewa gwamnatinsa ba za ta gajiya ba wurin rokon al'ummar jihar addu'o'i domin samun zaman lafiya.

Gwamna Bala ya bukaci addu'o'i daga al'umma

"Ba za mu gajiya ba wajen kira ga al’umma da su sanya jihar Bauchi da kuma Najeriya cikin addu’oinsu domin samun zaman lafiya da haɓakar tattalin arziki."
"Kada mu manta da tallafawa marasa ƙarfin cikin mu yayin bukukuwan Sallah."

- Bala Mohammed

Kara karanta wannan

Gwamna ya waiwayi ma'aikata, ya bayar da umarnin a tura masu kuɗi kafin Babbar Sallah

Gwamnan a karshe, ya yi addu'ar neman yardar ubangiji da amsar ibadun da ake yi.

Radda ya gwangwaje ma'aikata a Katsina

Kun ji cewa Gwamna Dikko Umaru Radda na jihar Katsina ya tallafawa ma'aikatan jiharsa da goron sallah.

Radda ya ba ma'aikata kyautar N15,000 domin gudanar da bukukuwan sallah cikin walwala tare da bashin N30,000.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel