Ana Tsaka da Shari’ar Sarautar Kano, Abba Ya Biya Wa Ɗalibai 119,903 Kudin NECO

Ana Tsaka da Shari’ar Sarautar Kano, Abba Ya Biya Wa Ɗalibai 119,903 Kudin NECO

  • Gwamnatin jihar Kano ta ware Naira biliyan 2.9 domin biya wa ɗalibai 119,903 kudin jarabawar NECO da NBAIS ta 2024
  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya ba da umarnin biyan kudin a wani yunkuri na tabbatar da cewa ƴaƴan talakawa sun yi karatu
  • Wasu daga al'umar Kano da Legit Hausa ta zanta da su, sun nuna godiyarsu ga gwamnan jihar kan wannan abin alkairi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince a fitar da Naira biliyan 2.9 domin a biya wa ƴaƴan talakawa kuɗin jarabawar NECO da NBAIS.

Akalla ɗalibai 199,903 da suka fito daga gidajen marasa galihu a faɗin jihar Kano ne za su amfana da tallafin kudin a shekarar 2024.

Kara karanta wannan

"Kuɗin sun yi yawa" Gwamnoni sun mayar da martani kan sabon mafi ƙarancin albashi

Gwamnatin Kano ta yi magana kan kudin NECO
Kano: Abba ya biya wa ɗalibai 119,903 kudin jarabawar NECO. Hoto: @Kyusufabba
Asali: Twitter

Sharaɗin biyan kuɗin jarabawar NECO a Kano

Kwamishinan ilimi na jihar, Dakta Umar Doguwa ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a yayin ganawa da manema labarai a Kano, in ji jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dakta Umar Doguwa ya ce za a zaɓi daliban da za a ba tallafin ne daga cikin waɗanda suka samu aƙalla makin 'C' a darusa huɗu a jarabawar gwaji ta 'Mock' da aka yi a kwanan baya.

Kwamishinan ilimin ya ce wannan na daga cikin kudurorin gwanatin Abba Yusuf na tabbatar da dalibai marasa galihu sun yi karatu mai zurfi.

Kano: Jajircewar Abba kan karatun ƴaƴan talaka

Rahoton ya nuna cewa gwamnatin jihar za ta biya wa kowane ɗalibi N24,250 kuɗin NECO da kuma N21,000 na kuɗin NBAIS.

Dakta Doguwa ya ce da farko an nemi a biya wa daliban da suka samu 'C' a darusa takwas kaɗai amma Abba ya ƙi yarda.

Kara karanta wannan

"Ya fi kowa hazaƙa": Gwamnan APC ya ba ɗalibin jami'a kyautar Naira miliyan 10

Kwanishinan ya ce gwamnan jihar ya ba da umarnin a biya kudin jarabawar ga duk ɗalibin da ya samu 'C' a darusa huɗu domin amfanar ƴaƴan talakawa masu yawa.

Jama'ar Kano sun yabawa Abba

A zantawar mu da Abba Hassan, daga karamar hukumar Gezawa ta Kano, ya jinjinawa gwamna jihar, Abba Kabir kan biya wa dalibai kudin jarabawar.

Abba Hassan ya ce tallafin gwamnan ya zo ne dai dai lokacin da al'uma ke fama da abin da za su ci ba wai ta biyan kudin makaranta ko wata jarabawa ba.

Sa'adatu Muhammad, malamar makaranta a Kano ta ce dalibai da dama ba su da halin biyan kudin wannan jarabawar, inda ta bayyana tallafin a matsayin 'ceton ilimin yara'.

Malamar makarantar ta yi kira ga wadanda za su sami tallafin da za su jajurce wajen ganin sun samu sakamako mai kyau a jarabawar domin nuna godiya ga Gwamna Abba Yusuf.

Kara karanta wannan

"Ya zama tarihi," Tinubu ya mayar da martani kan zargin dawo da tallafin fetur

An yi zaman shari'ar masarautar Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa babbar kotun tarayya da ke sauraron shari'ar rigimar masarautar Kano ta yi zama a ranar Alhamis tare da ɗaukar mataki.

A zaman kotun, lauyan gwamnatin jihar, Ibrahim Wangida ya shaida wa Alkali cewa ba su da hurumin sauraron wannan ƙarar, inda ya kafa misalai.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel