“Karancin Kudi”: Kungiyar ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki a Jami’ar Kano, Ta Bayyana Dalili

“Karancin Kudi”: Kungiyar ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki a Jami’ar Kano, Ta Bayyana Dalili

  • Kungiyar malaman jami'o'i (ASUU) reshen jami'ar Yusuf Maitama Sule da ke jihar Kano ta shiga yajin aikin gargadi na mako biyu
  • A cikin wata sanarwa daga shugabannin kungiyar, sun shiga yajin aikin ne saboda karancin kudin da suke samu daga gwamnati
  • A cewar kungiyar, gwamnatin jihar ta yi biris da duk wani kokari na ganin an zauna a teburin sasanci domin magance matsalar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano – Kungiyar malaman jami’a (ASUU) a jami’ar Yusuf Maitama Sule ta Kano, ta fara yajin aikin gargadi na tsawon mako biyu.

A baya dai kungiyar ta koka kan rashin kudi da jami'ar ke fama da shi yayin da gwamnatin jihar ta kashe biliyoyin Naira wajen tura dalibai zuwa karatu a jami’o’in kasashen waje.

Kara karanta wannan

'Yan haramtacciyar kungiyar IPOB sun budewa sojoji wuta, jami'an Najeriya sun mutu

Jami'ar Yusuf Maitama Sule da ke jihar Kano
Kano: ASUU ta fara yajin aiki a jami'ar Yusuf Maitama Sule. Hoto: Yusuf Maitama Sule University
Asali: Facebook

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa malaman sun ce jami’ar na dab da shiga fatara bayan shekaru ta na fama da karancin kudi daga gwamnatin jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

ASUU ta fara yajin aiki a Kano

A wata sanarwa dauke da sa hannun shugaba da kuma sakataren kungiyar ASUU, Mansur Sa’id da Yusuf Gwarzo, malaman sun ce har yanzu ba a magance koke-koken da suke yi na rashin kudi a jami’ar ba.

Kungiyar ta ce ta cimma matsayar ta na fara yajin aikin ne a taron da ta gudanar a ranar Laraba, 29 ga watan Mayu, in ji rahoton jaridar Independent.

Sanarwar ta kara da cewa:

Kungiyar ta amince da shiga yajin aikin gargadi na makwanni biyu, kuma idan ba a samu wani kwakkwaran alkawari daga gwamnati ba, malaman za su zarce da yajin aikin na dindindin.”

Kara karanta wannan

An kama mutumin da ake zargin yana kai wa 'yan bindiga makamai a Plateau

- ASUU, YUMSUK

Abin da ya jawowa ASUU shiga yajin aikin

A watan Nuwamban 2023, ASUU ta yi zargin cewa gwamnatin jihar ta yi watsi da bukatar ta na tattaunawa kan kalubalen da jami’ar ke fuskanta.

A cewar kungiyar, bukatun ta sun mayar da hankali ne kan bangarori uku da suka shafi: inganta yanayin aikin ma'aikata, isassun kudi, da kare 'yancin cin gashin kai da 'yancin karatun jami'ar.

Rigimar masarautar Kano da hukuncin kotu

A baya, Legit Hausa ta ruwaito cewa wasu umarni da kotuna biyu suka bayar kan rigimar masarautar Kano tsakanin Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero sun jawo rudani.

A yayin da babbar kotun tarayya ta bayar da umarnin a fitar da Sanusi II daga gidan sarauta, ita kuma babbar kotun jiha ta yi gargadi kan taba sabon sarkin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel