Hajjin 2024: Allah Ya Yiwa Wani Alhaji Daga Najeriya Rasuwa a Makkah

Hajjin 2024: Allah Ya Yiwa Wani Alhaji Daga Najeriya Rasuwa a Makkah

  • Allah ya yiwa ɗaya daga cikin alhazan Najeriya daga jihar Legas, Idris Oloshogbo rasuwa a Makkah bayan ya dawo daga ɗawafi
  • Babban sakataren hukumar jin daɗin alhazai na jihar, Saheed Onipede ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa ranar Laraba
  • Ya ce tuni aka yiwa marigayin janaza bisa dokokin da hukumomin Saudiyya suka shinfida, kana ya roƙi Allah ya gafarta masa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Rahotanni sun nuna cewa ɗaya daga cikin alhazan jihar Legas mai suna, Idris Oloshogbo, ɗan kimanin shekaru 68 a duniya ya rasu a ƙasa mai tsarki.

Likitocin ƙasar Saudiyya ne suka tabbatar da rasuwar Alhaji Oloshogbo a birnin Makkah.

Maniyyaci daga Legas ya rasu.
Jihar Legas ta rasaɗaya daga cikkn alhazanta a ƙasa mai tsarki Hoto: Inside The Haramain
Asali: Twitter

Makkah: Mai shirin zama Alhaji ya rasu

Kara karanta wannan

Hajj 2024: Bayan mutuwar Tawakaltu, wani Alhajin Najeriya ya mutu yana ibada a Saudiya

Jaridar Vanguard ta tattaro cewa Oloshogbo ya rasu ne jim kadan bayan ya dawo daga ɗawafin Ka’aba a Makkah.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Legas, Saheed Onipede, ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ta hannun mai magana da yawun hukumar, Taofeek Lawal a ranar Laraba.

A cewar Onipede, marigayin wanda ya fito daga karamar hukumar Shomolu a jihar Legas ya rasu ne a lokacin da yake cin abincinsa da yamma bayan Sallar Magriba.

Duk da har yanzu likitoci ba su bayyana asalin abin da ya zama ajalinsa ba, Onipede ya ce lamarin ba zai rasa alaƙa da hawan jini ba tare da lura da yadda ya jigata.

Gwamnatin Legas ta yi ta'aziyya

Ya kuma miƙa sakon ta'aziyya ga iyalai, ƴan uwa da abokan arzikin mamacin a madadin gwamnatin jihar Legas.

Kara karanta wannan

Hajjin 2024: An shiga jimami bayan rasuwar maniyyaciya daga Arewa a Saudiyya

Onipede ya roki Allah ya gafarta masa kura-kuransa, ya kuma ba shi Aljannar Firdausi da ladan aikin Hajji, tunda ya riga ya yi niyya, rahoton Tribune Nigeria.

Don haka ya yi kira ga sauran alhazai da su yi taka-tsan-tsan tare da kiyaye cikawa kansu aiki tun kafin a fara aikin Hajji na hakika wanda ya zama wajibi.

An yiwa mamacin jana'iza a Makkah

"An yi jana'izar marigayin a Makkah bisa ka'idojin da hukumomin Saudiyya suka shimfida," in ji Onipede.

Wani ma’aikacin hukumar, Waheed Shonibare ne ya jagoranci wasu jami’an gwamnatin jihar da wasu mahajjata wajen gudanar da sallar janaza ga mamacin a masallacin Ka'abah.

An biyawa yaro kuɗin hajji

A wani rahoton kuma an ji cewa an karrama yaron da ya nuna hadda da sanin ma'anonin Alkur'ani a jihar Kano da kujerar zuwa aikin Hajji.

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ce ta bayyana kyautar tare da fadi dalilai da suka sa aka karrama mahaddacin da damar sauke farali.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya ɗauki zafi, ya ba da umarnin a kama tsohon Sarkin Kano

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel