Dattawan Arewa Sun Yi Magana Kan Sake Naɗa Sanusi II a Matsayin Sarkin Kano

Dattawan Arewa Sun Yi Magana Kan Sake Naɗa Sanusi II a Matsayin Sarkin Kano

  • Dattawan Arewa sun nuna damuwa kan yadda ake ƙara samun yawaitar sauya sarakuna a jihar Kano da ke Arewa maso Yamma
  • Kungiyar dattawan NEF ta buƙaci gwamnatin Kano da waɗanda abin ya shafa su tafiyar da batun dawo da Sanusi II cikin kulawa da kwarewa
  • NEF ta kuma yi kira ga mutane su kwantar da hankulansu, kar su yarda su tada zaune tsaye kan abin da ke faruwa a jihar Kano

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Kungiyar dattawan Arewa (NEF) ta nuna matuƙar damuwa kan abubuwan da ke faruwa a jihar Kano, inda ake ta sauye-sauyen sarakuna a ƴan shekarun nan.

NEF ta bayyana cewa abin da ke faruwa a Kano babbar alama ce da ke nuna yadda sarakuna ke fuskantar ƙalubale a ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Sabon sarki: Matasa sun yi a zanga zanga, sun nemi Tinubu ya takawa Abba birki

Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II.
Dattawan Arewa sun nuna damuwa kan abubuwan da ke faruwa a masarautar Kano Hoto: Kano Emirate
Asali: Facebook

Har ila yau NEF ta nuna damuwa kan sauya Sarkin Kano da aka yi wanda ya haifar da fargaba a tsakanin mutane da ƴan Najeriya masu kishin ƙasa, rahoton Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ta kuma bukaci gwamnatin jihar Kano da ‘yan siyasa da abin ya shafa da su yi taka-tsan-tsan wajen tunkarar wannan batu mai muhimmanci domin hana tada zaune tsaye.

Idan ba ku manta ba a jiya Alhamis, gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano bayan rushe masarautu 5.

Gwamna Abba ya dawo da Sarkin Kano na 14 ne bayan majalisar dokoki ta sabunta dokar masarautu tare da tsige dukkan sarakuna biyar da Ganduje ya naɗa, cewar Premium Times.

NEF ta yi magana bayan naɗa Sanusi II

Da take mayar da martani kan haka, kungiyar datttawan Arewa (NEF) ta ce ya kamata dukkan bangarorin da abin ya shafa su tunkari lamarin cikin matukar kulawa da kwarewa.

Kara karanta wannan

Ana zargin shi ya shirya komai, Kwankwaso ya yi magana kan tsige sarakunan Kano

Mai magana da yawun NEF, Abdul-Azeez Suleiman ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rattaɓawa hannu.

"Ɗaukar matakin gaggawa da kalaman tunzura kan iya dagula al'amura kuma su kawo cikas ga zaman lafiya a jihar Kano," in ji NEF.

NEF ta buƙaci a zauna lafiya a Kano

Dattawan Arewa sun yi kira ga al'umma musamnan mazauna Kano su kwantar da hankulansu kana su zama masu bin doka da oda.

Sun jaddada cewa yana da matukar muhimmanci kar mutane su yi duk wani abu da zai iya kawo barazana ga zaman lafiya da tsaron jihar.

Sarki Sanusi ya shiga gidan gwamnatin Kano

Rahotanni sun nuna cewa Sarki Muhammadu Sanusi ya isa gidan gwamnatin jihar Kano da safiyar ranar Jumu'a, 24 ga watan Mayu, 2024.

Sarkin zai karɓi takadar mayar da shi kan kujerar sarautar Kano daga hannun Gwamna Abba Kabir Yusuf sannan ya wuce fadar Nasarawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel