NAHCON Ta Faɗi Dalilin Rashin Fara Jigilar Alhazan Kano da Wasu Jihohi 6, Ta Gama da Nasarawa

NAHCON Ta Faɗi Dalilin Rashin Fara Jigilar Alhazan Kano da Wasu Jihohi 6, Ta Gama da Nasarawa

  • Yau Laraba za a fara jigilar alhazan jihohin Kano, Kaduna da wasu jihohin Arewa zuwa ƙasa mai tsarki bayan kammala kwashe na Nasarawa
  • Hukumar NAHCON ce ta bayyana haka a wata sanarwa da Fatima Sanda Usara, mai magana da yawun hukumar ta rattaɓawa hannu
  • Ta shawarci maniyyata su kwantar da hankalinsu domin duk wanda ya fara tafiya shi zai fara dawowa gida bayan kammala aikin hajji

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) ta sanar da cewa ta kammala jigilar maniyyatan jihar Nasarawa zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara ta fitar fitar ranar Laraba, 22 ga watan Mayu, 2024.

Kara karanta wannan

NSCDC ta damke mai safarar mutane a Kano, wasu sun tsere

Jigilar alhazai.
Za a fara kwashe alhazan Kano, Kaduna da wasu jihohi zuwa Saudiyya yau Laraba Hoto: NAHCON
Asali: Facebook

Ta ce maniyyatan jihohin Kaduna, Kano, Borno, Yobe da Adamawa za su fara tashi zuwa ƙasa mai tsarki yau Laraba, kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Abin farin ciki, jihar Nasarawa ce ta farko da ta kammala jigilar maniyyatan ta 1,794 zuwa ƙasa mai tsarki domin gudanar da aikin Hajjin bana 2024.
"Jiya Talata da daddare ake tsamnanin jihar Oyo da hukumomin tsaro za su kammala kwashe maniyyatan su, sawu ɗaya ya rage ma kowanen su."

- Fatima Usara.

Za a fara kwashe alhazan Kano da Kaduna

Mai magana da yawun NAHCON ta ƙara da cewa a halin yanzun za a shiga mako na biyu bayan fara jigilar alhazan Najeriya zuwa Saudi Arabia.

Ta ce jihohin da za su fara jigilar alhazan su yau Laraba sun hada da jihohin Kaduna, Yobe, Kano, Adamawa, Borno, da Sokoto da kuma Filato.

Kara karanta wannan

Sanatan Kebbi ya faɗi gwamnan Arewa da ke biyan sojoji N500m duk wata saboda tsaro

Hukumar ta kuma buƙaci maniyyatan da su kwantar da hankalinsu kan rashin kwashe su da wuri domin NAHCON tana da tsarin na farkon tafiya shi ne na farko a dawowa.

Fatima ta ce kowane maniyyaci zai kwashe kwanaki daidai da kowa a ƙasa mai tsarki, babu wanda zai fi wani.

Ta kuma ƙara da cewa NAHCON ta samu nasarar jigilar alhazai sama da 10,000 kawo yanzu kuma babu jirgin da aka soke bayan kammala shirin tashinsa.

Naira ta kara farfaɗowa

A wani rahoton kuma, an ji kimar Naira ta ƙara sama a kasuwar hada-hadar gwamnati ranar Talata sa'o'i 24 bayan kuɗin Najeriya sun rikita Dalar Amurka.

Rahoton FMDQ na ranar Talata ya nuna cewa Naira ta tashi da N3.31 inda aka yi musayar kowace Dalar Amurka kan N1,465.68.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel