Sabon Shugaban Senegal, Faye Ya Sanya Labule da Tinubu a Fadarsa, Bayanai Sun Fito

Sabon Shugaban Senegal, Faye Ya Sanya Labule da Tinubu a Fadarsa, Bayanai Sun Fito

  • Matashin sabon shugaban kasar Senegal, Bassirou Faye ya kawo ziyara Najeriya kasa da watanni biyu a kan karagar mulki
  • Faye ya iso fadar shugaban kasar Najeriya da misalin karfe 3:09 da ranar yau Alhamis 16 ga watan Mayu a birnin Abuja
  • Wannan na zuwa ne bayan rantsar da shugaban mai shekaru 44 a watan Afrilu bayan lashe zaben shugaban kasa a Senegal

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Sabon shugaban Senegal, Bassirou Diomaye Faye ya iso fadar shugaban kasar Najeriya, Bola Tinubu a Abuja.

Bassirou Faye ya ziyarci Bola Tinubu a karon farko tun bayan hawa karagar mulki a farkon watan Afrilun wannan shekara.

Kara karanta wannan

Dan majalisar PDP ya nemi Tinubu ya fara tafiye tafiye a mota ko ya hau jirgin haya

Shugaban Senegal, Faye yana ganawa da Tinubu Abuja
Shugaban Senegal, Bassirou Faye kawo ziyara fadar Shugaba Bola Tinubu. Hoto: @DOlusegun.
Asali: Twitter

Faye ya kawowa Tinubu ziyara karin farko

Matashin shugaban ya iso fadar Aso Rock da misalin karfe 3:09 a yau Alhamis 16 ga watan Mayu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bassirou mai shekaru 44 ya kafa tarihi a kasar inda ya kasance mafi karancin shekaru a jerin shugabannin Sanagal.

Idan an tuna, Faye ya samu 54% na kuri'un da aka kada a zaben kasar da aka gudanar a watan Maris din wannan shekara.

Faye ya samu tarba daga Tinubu

Hadimin shugaban a bangaren kafofin sadarwar zamani, Dada Olusegun ya tabbatar da haka a shafinsa na X.

Olusegun ya ce tuni aka riga aka shirya tarbar sabon shugaban kasar a fadar Aso Rock cikin kayatarwa.

"Fadar shugaban kasa a Abuja cike ake da murna da kuma shirye-shiryen tarbar shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye a fadar Aso Rock."

Kara karanta wannan

Yayin da ake kukan tsadar kujerar hajji, Tinubu ya tausaya da tallafin biliyoyi

- Dada Olusegun

Faye shi ne shugaban kasar Senegal na biyar da aka zaba wanda aka rantsar da shi a ranar 2 ga watan Afrilun 2024.

Tinubu ya tallafa a aikin hajji

A wani labarin, kun ji cewa Shugaban kasa, Bola Tinubu ya ba da tallafi domin rage tsadar kujerun aikin hajjin bana.

Mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima shi ya tabbatar da haka a jiya Laraba 15 ga watan Mayu a birnin Kebbi.

Shettima ya ce Tinubu ya tallafa da kudin ne domin rage wa maniyyata tsadar kujerar inda ya ce ya himmatu wurin inganta Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel