'Yan Bindiga Sun Ga Takansu Yayin da Suka Yi Yunƙurin Kai Farmaki a Jihar Kaduna
- Dakarun rundunar sojojin Najeriya sun halaka ɗan bindiga a yankin ƙaramar hukumar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna
- Gwarazan sojojin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar ne yayin da suke hanyar zuwa kai hari kan mutanen da ba su ji ba kuma ba su gani ba
- A cewar rundunar sojin yanzu haka jami'ai sun bi bayan maharan da nufin kamo su domin su girbi abin da suka shuka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Kaduna - Jami'an rundunar sojojin Najeriya sun kashe ɗan bindiga ɗaya yayin da suke hanyar zuwa kai hari a titin Birnin Gwari a jihar Kaduna.
Tawagar miyagun ƴan bindigar sun fito da nufin zuwa kai hari, kwatsam sojoji suka masu kwantan ɓauna suka hallaka ɗan bindiga ɗaya.
![Sojojin Najeriya. Sojojin Najeriya.](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/b71f2e79dccf40a6.jpg?imwidth=900)
Asali: Facebook
Rundunar sojojin ƙasa ta Najeriya ta tabbatar da samun wannan nasara a shafinta na manhajar X wanda aka fi sani da Twitter a ranar Laraba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sojoji sun gwabza da ƴan bindiga
Sojojin sun yi wa 'yan bindigar kwanton bauna a kewayen kauyen Kwaga, inda suka kashe daya yayin da sauran suka gudu ɗauke da raunuka.
An tattaro cewa tawagar ƴan bindigar sun yi kaurin suna wajen yawan kai hare-hare kan bayin Allah a ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.
Sanarwar rundunar sojojin ta ƙara da cewa ɗaukin da gwarazan sojojin suka kai ya zama silar hana ƴan bindigar kai farmaki kan mutane a yankin.
Dakarun sojojin sun kuma kwato bindigu kirar AK-47 guda biyu da magazines, da kuma babura biyu a lokacin arangama da ƴan ta'addan.
Sanarwan ta ƙara da cewa, "Yanzu haka jami'an sojojin sun bazu neman ƴan bindigar da nufin kama su."
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/cc6ed74cb552a783.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Jami'an tsaro sun yi musayar wuta da ƴan bindiga, sun samu gagarumar nasara a Katsina
Sojoji sun kashe hatsabibin ɗan bindiga
Wannan na zuwa ne kwanaki kalilan bayan sojoji sun yi nasarar kashe ƙasurgumin ɗan bindiga da ya addabi al'umma, Dogo Bagaje a jihar Kaduna.
Lamarin ya faru a karamar hukumar Giwa da ke jihar inda aka tafka mummunan faɗa wanda ya yi sanadin mutuwar Bagaje da wasu miyagun 'yan bindigan.
Mutum 8 sun mutu a harin masallacin Kano
A wani rahoton kun ji cewa wasu ƙarin mutum bakwai daga cikin waɗanda suka samu rauni a harin masallaci a jihar Kano sun riga mu gidan gaskiya.
Hakan ya sa adadin waɗanda suka mutu a harin ya zama mutum takwas yayin da sauran mutane 17 ke kwance a asibitin Murtala Muhammad
Asali: Legit.ng