Matsin Rayuwa Ya Tsananta, Izala Ta Umarci Masallatai a Fara Al Kunut
- Kungiyar Jama'atu Izatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah ta sanar da fara al-kunut kan halin kuncin da Najeriya ke ciki
- Shugaban kungiyar na jihar Gombe, Alhaji Salisu Muhammad Gombe ne ya bayar da sanarwar yayin wani taro da suka gudanar
- Shugaban har ila yau ya yi bayanai na musamman kan malaman da suka gudanar da tafsiri a watan azumin da ya wuce
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Gombe - Biyo bayan halin tsadar rayuwa da ake ciki a Najeriya, kungiyar Jama'atu Izatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah ta sanar da fara al-kunut domin neman sauki.
![Jibwis NG Jibwis NG](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/bc516ffb3532759b.jpg?imwidth=900)
Asali: UGC
Daga ina umurnin Izala ya fito?
Shugaban kungiyar na jihar Gombe, Alhaji Salisu Muhammad Gombe ne ya bada umurnin yayin wani taro da kungiyar ta shirya.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/e02a207fa40cfe8a.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Jami’an Birtaniya sun yi watsi da Yarima Harry a ziyarar da ya kawo zuwa Najeriya
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Rahoton jaridar Aminiya ya nuna cewa umurnin ya shafi masallatan kungiyar ne da ake sallolin yau da kullum guda biyar a fadin Gombe.
Shugaba Salisu ya bayar da umarnin ne a yayin taron tattara rahoton yadda tafsirin Ramadan ya gudana a jihar Gombe.
Izala ta fadi dalilin fara Al-kunuti
Cikin dalilan da shugaban ya bayar sun hada da tsadar kayayyaki da suka jefa al'umma da dama cikin kuncin rayuwa.
Ya kara da cewa suna fata yin al-kunut zai sa Madaukakin Sarki Allah SWT ya kawo dauki kan halin da Najeriya ke ciki.
Jawabi kan tafsirin Ramadan
Haka zalika a lokacin taron kungiyar ta tattauna kan yadda take gudanar da ayyukan ta a dukkan yankunan jihar.
Shugaban ya kuma mika godiya ga malaman da suka gabatar da tafsiri a wurare sama da 60 a fadin jihar.
Izala ta yi martani kan kashe malami
A wani rahoton, kun ji cewa yayin da ake jimamin kisan gillar da aka yi wa Sheikh Hassan Mada a Zamfara, kungiyar Izala ta yi martani kan lamarin.
Kungiyar ta zargi jami'an CPG da hannu a kisan da aka yi wa shugaban majalisar malaman birnin Gusau da ke Zamfara bayan kama wasu 'yan banga 10 da zargin su na da hannun a kisan da aka yi wa shehin malamin.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng