Rundunar Sojoji Ta Dauki Mataki Kan 'Yan Ta'addan da Suka Farmaki Jami'anta a Borno
- Rundunar sojojin Najeriya ta sanar da hallaka ƴan ta'adda shida da suka farmaki jami'anta a jihar Borno
- Ƴan ta'addan sun yi wa sojojin kwanton ɓauna ne inda suka hallaka Laftanar ɗaya tare da raunata wasu sojoji huɗu
- Biyo bayan aukuwar lamarin an aika da ƙarin jami'ai inda suka yi artabu da ƴan ta'addan tare da fatattakarsu daga maɓoyarsu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Borno - Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa ta kashe ƴan ta’adda shida da suka kashe jami’anta a hanyar Biu-Buni-Yadi, a jihar Borno.
Ƴan ta'addan dai sun farmaki jami'an sojojin ne bayan sun yi musu kwanton ɓauna a kan hanyar.
![Sojoji sun hallaka 'yan ta'adda Sojoji sun hallaka 'yan ta'adda](https://cdn.legit.ng/images/1120/53bda1adc4fd6ced.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Rundunar ta ce bayan aukuwar lamarin, an aika da ƙarin sojoji inda suka tarwatsa maɓoyar ƴan ta'addan a cikin Timbuktu Triangle, cewar rahoton jaridar Daily Trust.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/64dfc0b23ad3b50d.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
'Yan bindigan da suka sace dalibai a Arewa sun bayyana kudin fansan da za a ba su
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Me rundunar sojoji ta ce kan lamarin?
Daraktan yaɗa labarai na rundunar, Edward Buba, shi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi, inda ya ce Laftanar guda ɗaya kawai aka kashe a yayin kwanton ɓaunan.
Manjo-Janar Buba, ya ce sauran sojoji huɗu da suka samu raunuka, ana ci gaba da ba su magani a asibiti, rahoton jaridar PM News ya tabbatar.
A kalamansa:
“A ranar 5 ga watan Afrilu da misalin ƙarfe 09:35 na safe, dakarun Operation Hadin Kai, sun fuskanci kwanton ɓauna na ƴan ta'adda a hanyar Buratai-Buni-Yadi.
"Abin baƙin ciki, a yayin fafatawar an kashe Laftanar guda ɗaya. Yayin da wasu sojoji huɗu suka samu raunuka inda ake duba lafiyarsu a asibiti.
"Dakarun sojojin da aka ƙara aikawa sun bi ƴan ta’addan har zuwa maɓoyarsu a cikin Timbuktu Triangle tare da yin musayar wuta."
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/0a5e22ab7c7ff9b5.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Bayan abin da ya faru a Delta 'yan ta'adda sun sake yi wa sojoji kwanton bauna, an rasa mutum 6
"Sojojin sun yi nasarar kashe shida daga cikin ƴan ta’addan tare da ƙwato bindigu ƙirar AK 47 guda biyar da harsashi na musamman mai kaurin 7.62mm guda 103."
- Janar Edward Buba
Sojoji sun hallaka ƴan ta'adda
A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka tantiran ƴan ta'adda guda uku a jihar Kaduna.
Sojojin sun sheƙe ƴan ta'addan ne bayan sun yi musu kwanton ɓauna lokacin da suke kan hanyar kai gyaran baburansu.
Asali: Legit.ng