Kisan sojoji: Rundunar Sojoji Ta Saki Sunaye da Hotunan Mutum 7 da Ake Nema Ido Rufe

Kisan sojoji: Rundunar Sojoji Ta Saki Sunaye da Hotunan Mutum 7 da Ake Nema Ido Rufe

  • Dakarun sojoji a Najeriya sun sanar da mutane takwas da suke nema ruwa a jallo kan kisan sojoji a jihar Delta
  • Rundunar ta fitar da sunayen mutanen ne da suka hada da wani Farfesa da wata mata da sauran mutane shida
  • Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa sa daraktan yada labarai na rundunar, Manjo-janar Edward Buba ya fitar

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Rundunar sojojin Najeriya ta fitar sunayen mutane takwas da ta ke nema ruwa a jallo.

Rundunar ta fitar da sunayen ne kan zarginsu da kisan sojoji 17 a kauyen Okuama da ke jihar Delta.

Sojoji sun fitar da sunayen mutane 8 da suke name ruwa a jallo kan kisan jami'ansu
Rundunar sojoji ta na neman wani Farfesa da mutum 7 kan kisan sojoji a Delta. Hoto: @HQNigerianArmy.
Source: Twitter

Sunayen wadanda sojojin ke nema

Kara karanta wannan

Kisan sojoji 17: Tinubu ya fusata, ya ba da sabon umarni ga dattawa da sarakunan Okuama

Daga cikin wadanda ake neman akwai Farfesa Ekpekpo Arthur da wata mata, Igoli Ebi da Reuben Baru da Akata Malawa David.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran sun hada da Sinclear Oliki da Clement Ikolo da Dennis Bakriri da kuma Daniel Omotegbono.

Daraktan yada labaran rundunar, Manjo-janar Edward Buba shi ya tabbatar da haka a shafin Facebook a yau Alhamis 28 ga watan Maris.

Sai dai Buba ya ce babu wani kudi da aka saka a matsayin tukuici ga wadanda suka kawo su ko kuma ba da bayanai da za su taimaka a cafke su.

Yadda aka hallaka sojoji 17 a Delta

Wannan sanarwa daga rundunar na zuwa ne bayan kisan wasu sojoji 17 a jihar Delta da ke Kudu maso Kudancin Najeriya.

Sojojin sun gamu da ajalinsu ne yayin da suka je kwantar da tarzoma a kauyen Okuama da ke karamar hukumar Ughelli ta Kudu a jihar.

Kisan sojojin ya ta da ƙura inda wasu ke kiran a dauki mummunan mataki kan haka saboda dakile faruwar hakan a nan gaba.

Kara karanta wannan

Bassirou Faye: Abubuwa 6 da ya kamata ku sani kan sabon shugaban Senegal mai jiran gado

Tinubu ya ba dattawa Okuama umarni

Kun ji cewa shugaban kasa, Bola Tinubu ya umarci dattawa da sarakunan kauyen Okuama a jihar Delta sa su zakulo wadanda ake zargi da kisan sojoji 17.

Tinubu ya bayyana haka ne a jiya Laraba 27 ga watan Maris a Abuja yayin jana'izar sojojin da suka mutu.

Shugaban ya ce ba zai taba bari rayukansu ya tafi a banza ba inda ya ce dole a bi musu hakkinsu wurin tabbatar da hukunta masu laifin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.