Rundunar 'Yan Sanda Ta Bazama Neman Fitaccen Malamin Musulunci Ruwa a Jallo, Bayanai Sun Fito

Rundunar 'Yan Sanda Ta Bazama Neman Fitaccen Malamin Musulunci Ruwa a Jallo, Bayanai Sun Fito

  • Rundunar 'yan sanda a jihar Bauchi ta sanar da neman fitaccen malamin addinin Musulunci ruwa a jallo
  • Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a yau Alhamis 8 ga watan Faburairu a Bauchi
  • Sanarwar ta ce ofishin kwamishinan 'yan sanda a jihar na neman Sheikh Idris saboda raina umarnin kotu da ya yi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Bauchi - Rundunar 'yan sanda a jihar Bauchi ta sanar da neman fitaccen malamin addinin Musulunci a jihar.

Rundunar ta ayyana neman Dakta Abdul'aziz Idris Dutsen Tanshi ruwa a jallo a yau Alhamis 8 ga watan Faburairu.

Rundunar 'yan sanda na neman shehin malamin Musulunci ruwa a jallo
Rundunar 'yan sanda a Bauchi ta sanar da neman Sheikh Abdul'aziz Dutsen Tanshi ruwa a jallo. Hoto: Idris Abdul'aziz.
Asali: Facebook

Wane umarni rundunar ta bayar?

Kara karanta wannan

Mahara sun sake hallaka fitaccen basarake a jihar Arewa, bayanai sun fito

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Alhamis 8 ga watan Faburairu a Bauchi, cewar Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce ofishin kwamishinan 'yan sanda a jihar na neman Sheikh Idris saboda raina umarnin kotu da ya yi a baya.

Rundunar ta ce adireshinsa shi ne Dutsen Tanshi kuma ɗan shekaru 63, siriri kuma ya na yawan saka kayan Hausawa.

Mene ake zargin malamin a kai?

Ta kuma bukaci duk wanda ya ke da bayanan da zai sa a kai ga nasarar kama malamin ya tuntubi hukumar.

Idan ba a manta ba, shehin malamin ya na fuskantar shari'a a gaban kotun shari'ar Musulunci da ke Bauchi.

A baya, an ba da belinsa amma ya ki halartar zaman kotun har guda biyu don ci gaba da sauraran karar.

Kara karanta wannan

Sufetan 'yan sanda ya shiga babbar matsala, an fara farautarsa akan aikata kisan kai

Hakan ya tilasta kotun ba da umarnin cafke malamin saboda kin mata biyayya.

Kotu ta ba da umarnin cafke malamin Musulunci

Kun ji cewa kotun shari'ar Musulunci a jihar Bauchi ta ba da umarnin cafke Sheikh Idris Abdul'aziz Dutsen Tanshi.

Ana zargin shehin malamin addinin, Sheikh Abdul'aziz da kin mutunta umarnin kotun kan halartar zamanta da aka yi har sau biyu.

Wannan na zuwa ne bayan Shehin malamin ya ki halartar zaman kotun har sau biyu da aka yi a ci gaba da sauraran karar tasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.