Kano: Ana Rade-radin Tube Shi a Sarauta, Ado Bayero Zai Kaddamar da Gagarumin Aiki Don Talaka

Kano: Ana Rade-radin Tube Shi a Sarauta, Ado Bayero Zai Kaddamar da Gagarumin Aiki Don Talaka

  • Ana cikin cece-kuce kan matsayin kujerar Sarkin Kano, Ado Bayero zai kaddamar da wani gagarumin aiki a jihar
  • Sarkin zai kaddamar da asibitin kungiyar Musulunci ta Ahmadiyya Muslim Jama’at a birnin Kano
  • Kaddamar da sabon asibitin zai gudana ne a gobe Asabar 20 ga watan Janairu wanda zai iya daukar marasa lafiya 100 a rana

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero zai kaddamar da sabon asibitin Ahmadiyya Muslim Jama’at a birnin Kano.

Kaddamar da sabon asibitin zai gudana ne a gobe Asabar 20 ga watan Janairu wanda zai iya daukar marasa lafiya 100 a rana, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun kai hari kauyen Zariya, sun sace uwa da ɗanta, mijin ya tsere

Sarkin Kano zai kaddamar da gagarumin aiki don talaka a jihar
Ado Bayero zai kaddamar bude sabon asibiti a Kano. Hoto: Aminu Ado Bayero.
Source: Facebook

Mene Sarkin Kano, Ado Bayero zai kaddamar a Kano?

Asibitin da ke kan hanyar Kano zuwa Maiduguri har ila yau, Sarkin ne ya kaddamar da kafa tubalin gina asibitin a watan Yulin shekarar 2021.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda kungiyar Musuluncin ta ce a cikin wata sanarwa, Sarkin zai samu rakiyar sarakuna da ke yankinsa, World Top News ta tattaro.

Sauran wadanda ake sa ran za su halarci taron sun hada da masu mukamai a gwamnatin jihar da Tarayya da FRSC da kuma hukumar NDLEA.

Kiraye-kirayen da ake yi a Kano kan tube Sarkin Kano

Kungiyar Musulunci ta Ahmadiyya Muslim Jama’at ta gina asibitinta na farko a shekarar 1950 a Apapa da ke Legas da kuma Kano a shekarar 1962.

Wannan na zuwa ne yayin da ake ta cece-kuce kan ruguza masarautun Kano da tsohon gwamnan jihar, Abdulllahi Ganduje ya kirkiro.

Kara karanta wannan

Gyadar dogo: Mutanen da suka sha da kyar da aka kifar da Gwamnatin Najeriya a 1966

Kiraye-kirayen mayar da tsohon Sarki, Sunusi Lamido sun fara tasiri wanda idan hakan ta tabbata zai maye gurbin Sarki Aminu Ado Bayero.

Da alamu Sunusi Lamido zai koma kujerarsa

A wani labarin, ana ta kiraye-kirayen mayar da tsohon Sarkin Kano, Sunusi Lamido Sunusi kan kujerarsa.

Kiraye-kirayen sun fara tasiri a jihar tun bayan cin zaben Gwamna Abba Kabir a matsayin gwamnan jihar a watan Maris.

Wannan ya biyo bayan tabbatar da nasarar Gwamna Abba Kabir a matsayin halastaccen gwamnan jihar a Kotun Koli.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.