Motsi Ya Fi Labewa: Dattawa 250 a Jihar Katsina Sun Samu Tallafi Daga Uwar Gidan Shugaba Tinubu

Motsi Ya Fi Labewa: Dattawa 250 a Jihar Katsina Sun Samu Tallafi Daga Uwar Gidan Shugaba Tinubu

  • Uwar gidan shugaban kasa Tinubu ta sanya farin ciki a zukatan dattawa 250 a jihar Katsina bayan ba su tallafin naira dubu 100 duk mutum daya
  • Tallafin naira dubu 100 na daga cikin shirin uwar gidan shugaban kasar na tallafawa dattawa 250 a kowacce jihar Najeriya
  • Wannan tallafin zai taimaka wajen rage radadin wahalar da dattawan suka shiga sakamakon janye tallafin man fetur da Tinubu ya yi

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Jihar Katsina - Dattawa 250 ne a jihar Katsina suka amfana da tallafin naira dubu 100 daga shirin uwar gidan shugaban kasar Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu.

Wannan tallafin na daga cikin shirye-shiryen Sanata Oluremi Tinubu na bunkasa rayuwar dattawa a kasar da zai cimma muradin "sabuwar Najeriya".

Kara karanta wannan

Kotu ta garkame matasa 2 kan kashe abokinsu saboda shinkafa

Uwar gidan Tinubu ta tallafawa dattawa 250 a Katsina
Sanata Oluremi Tinubu, uwar gidan Tinubu ta tallafawa dattawa 250 a Katsina da naira dubu 100 duk mutum daya. Hoto: Mobile Media Crew
Asali: Twitter

Manufar shirin ba dattawa tallafin N100,000 a jihohin Najeriya

Dattawan da suka amfana da tallafin sun nuna matukar farin ciki yayin da suka karbi kudin karkashin shirin da zai tallafawa dattawa 250 a kowacce jihar Najeriya. TVC News ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Uwar gidan gwamnan jihar Katsina Zulaiha Dikko Umar Radda wacce ta wakilci uwar gidan shugaban kasar ta karfafi guiwar dattawan tare da nuna masu muhimmancinsu a cikin jama'a.

The Nation ta rahoto uwar gidan shugaban kasar na rokon dattawan da su mayar da hankali wajen kula da lafiyarsu da kuma komawa ga Allah don neman lahirarsu.

Tun bayan zuwan gwamnatin Tinubu, ta mayar da hankali wajen bunkasa rayuwar jama'a musamman biyo bayan janye tallafin man fetur da shugaban kasar ya yi.

Tinubu ya dawo da shirin ciyar da dalibai abinci, ya fadi dalili

Kara karanta wannan

Gwamnan APC ya rabawa ma'aikata N100,000 don bikin kirsimeti

A wani labarin kuma, shugaban kasa Bola Tinubu ya dawo da shirin ciyar da dalibai abinci don bunkasa ilimi da rage yawan yara masu gararamba a gari.

Idan ba a manta ba, tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ne ya kawo shirin ciyar da abincin, amma ya dakatar da shi bayan dogon lokacin da aka yi ana gudanar da shi.

Sai dai Tinubu ya yi wa shirin garambawul, inda ya dauke shi daga ma'aikatar jin kai zuwa ma'aikatar ilimi don tabbatar da cewa ba a samu wata matsala ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.