Shugaba Tinubu Ya Naɗa mutum 11 a Kotun Koli Ana Dab da Yanke Hukunci kan Zaben Gwamnan Kano

Shugaba Tinubu Ya Naɗa mutum 11 a Kotun Koli Ana Dab da Yanke Hukunci kan Zaben Gwamnan Kano

  • Bola Ahmed Tinubu ya aike da wasika zuwa majalisar dattawa, inda ya nemi ta amince da naɗin sabbin alkalai 11 na kotun koli
  • Shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya karanta sakon Tinubu wanda ke kunshe da sunayen alƙalai 11
  • Wannan mataki na zuwa ne kwana ɗaya gabanin kotun koli ta yi zaman sauraron ƙarar zaben gwamnan Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci majalisar dattawan Najeriya ta amince da naɗin sabbin alƙalai 11 da zasu koma aiki a kotun koli.

Shugaba Tinubu ya nemi amincewa da sabbin alkalan ne a wata wasiƙa da ya aike wa majalisar dattawan, kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Shugaban majalisar dattawa ya ayyana kujerun sanatoci 2 a matsayin babu kowa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Tinubu ya nemi majalisar dattawa ta amince da nadin alkalan kotun koli 11 Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Facebook

Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ne ya karanto wasiƙar buƙatar Shugaba Tinubu a zaman sanatoci na ranar Laraba, 20 ga watan Disamba, 2023.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin wasiƙar, Shugaba Tinubu ya ce buƙatar naɗin alkalan ta yi daidai da tanadin sashe na 231(2) na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima).

Sunayen alƙalai 11 da aka naɗa a kotun ƙoli

Ya kuma jero sunayen alkalan da yake bukatar naɗawa a kotun koli, wanda suka kunshi, mai shari'a Jummai Sankey, mai shari'a Stephen Adah, da mai shari'a Mohammed Idris.

Sauran sun haɗa da mai shari'a Haruna Tsammani, mai shari'a Jamilu Tukur, mai shari'a Abubakar Umar, mai shari'a Chidiebere Uwa, da mai shari'a Chioma Nwosu-Iheme.

A rahoton Vanguard, ragowar sunayen waɗanda Tinubu ya naɗa a kotun Allah ya isa sune, mai shari'a Obande Ogbuinya, mai shari'a Moore Adumein da kuma mai shari'a Habeeb Abiru.

Kara karanta wannan

Daga Karshe, yan majalisar dokoki sun ɗauki sabon mataki ƙan yunkurin tsige gwamnan PDP

A gobe Alhamis ne kotun kolin Najeriya ta tsara sauraron shari'ar zaben gwamnan Kano tsakanin Abba Kabir Yusuf na NNPP da Yusuf Gawuna na APC.

FG zata magance matsalar tsaro a 2024

A wani rahoton kuma Gwamnatin tarayyan Najeriya ta lashi takobin murkushe matsalar tsaro gaba ɗaya daga nan zuwa 2024.

Ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle, ne ya bayyana haka a wata hira da BBC Hausa wadda aka wallafa ranar Talata, 19 ga watan Disamba, 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262