Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Babbar Kungiya a Abuja a Bayan Gidan Tinubu
- Kakakin rundunar ƴan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta mayar da martani kan harin da wasu ƴan bindiga suka kai a Abuja
- Adeh ta bayyana cewa iyalansa ba su kai rahoton sace John Emmanuel a ofishinsu ba, don haka ƴan sanda ba su ɗauki mataki ba
- A halin da ake ciki, matar mutumin ta bayyana cewa masu garkuwa da mutanen suna neman naira miliyan 15 a matsayin kuɗin fansa kafin shugaban jaridar ya samu ƴancinsa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - An yi garkuwa da shugaban ƙungiyar dillalan jaridu ta birnin tarayya Abuja, John Emmanuel.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa ƴan bindiga sun yi garkuwa da Mista Emmanuel ne a hanyarsa ta komawa gida, a unguwar Giri da ke babban birnin tarayya Abuja a daren ranar Talata, 12 ga watan Disamba.

Asali: Facebook
Masu garkuwa da mutanen sun buƙaci iyalansa da su biya Naira miliyan 15 a matsayin kudin fansa, domin ya shaƙi iskar ƴanci.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Matar mutumin, Mrs Uche Emmanuel, a ranar Laraba, 13 ga watan Disamba, a wata hira, ta tabbatar da sace mijinta yayin da ta kuma bayyana cewa waɗanda suka sace shi sun kira suna neman kuɗin fansa domin ya samu ƴanci.
A kalamanta:
"Eh, an sace mijina a Giri ranar Talata da misalin ƙarfe 8:00 na dare. Yana cikin motar tasi ne a hanyarsa ta komawa gida, abin takaici, motar ta miyagu ce, kuma suna neman Naira miliyan 15 kafin su sake shi."
Ƴan sanda sun mayar da martani
A halin da ake ciki, rundunar ƴan sandan babban birnin tarayya Abuja ta ce har yanzu ba a kai rahoton lamarin ga ƴan sanda domin su ɗauki mataki ba.

Kara karanta wannan
'Yan bindiga sun kutsa kai cikin Abuja, sun tafka mummunar ɓarna tare da kashe jami'in tsaro
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, sai ta kada baki ta ce:
"Har yanzu babu rahoton wannan lamarin da aka kai a ofisoshin mu. Wataƙila iyalan ba su tuntuɓe mu ko kai rahoto gare mu (ƴan sanda) ba tukunna, ba za mu iya sanin abin da ba a sanar da mu ba."
Ƴan Bindiga Sun Halaka Sojoji a Rivers
A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu miyagun ƴan bindiga sun halaka sojoji huɗu a yayin wani kwanton ɓauna a jihar Rivers.
Ƴan bindigan dai sun yi kwanton ɓauna ne yayin da sojojin ke raka wani ayarin motocin wani kamfanin mai zuwa jihar Bayelsa.
Asali: Legit.ng