Hadiman ’Yan Majalisar Dokokin Najeriya Sun Koka Kan Rashin Biyansu Albashin Watanni 15

Hadiman ’Yan Majalisar Dokokin Najeriya Sun Koka Kan Rashin Biyansu Albashin Watanni 15

  • Hadiman majalisar da suka yiwa su Femi Gbajabiamila hidima sun koka kan rashin samun albashin watanni sama 15
  • An bayyana yadda gwamnati da hukumar gudanarwar majalisar dokokin Najeriya suka gaza biyan albashin watannin
  • Ba wannan ne karin farko da ake bayyana rashin biyan albashin ma'aikata ba a kasar nan, ana yawan samun irin haka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Salisu Ibrahim kwararren editan fasaha, kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas.

FCT, Abuja - Hadiman 'yan majalisar tarayya dokokin Najeriya sun roki shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya baki a biya su albashinsu na watanni 15 da suke bin gudanarwar majalisar.

Hakazalika, sun yi kira ga sauran hukumomin yaki da rashawa irinsu EFCC da ICPC da su yi kokarin bincika wannan lamarin, The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Dakarun Najeriya sun kama ’yan ta’adda 122, sun ceto mutane 189 cikin mako daya, DHQ

Yadda aka ki biyan hadiman majalisa albashin watanni 15
Ba a biya hadiman majalisa albashin watanni 15 ba | Hoto: @SenatorLawan, @femigbaja
Asali: Twitter

A bangarensu, sun yanke shawarin yin azumi da addu'o'i na musamman domin rokon Allah ya ba su nasarar samun albashinsu daga hannun gwamnati.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wadanda aka yiwa hidimar watanni 15

Wata sanarwar da aka fitar a ranar Juma'a mai dauke da sa hannun Sulaiman Abbas da Joseph Isa ta ce:

“Ma’aikatan da suka bar ofis a watan Yuni 2023, sun aikin Majalisar ne a watan Mayu, 2021, bayan sun yi aiki a matsayin hadiman ‘yan majalisa na tsawon shekaru biyu, sun sha fama da yunwa na tsawon watanni 15 daga cikin watanni 24 da suka yi suna hidima."

'Yan majalisar da aka yiwa hidima sun hada da tsohon shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawal da kuma na majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, rahoton Punch.

Hakazalika, akwai sauran 'yan majalisar da suka shude a majalisa ta 9 da aka ce an yi musu hidimar da gudanarwar majalisar dokokin kasar bata biya ba.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Alkali ya umurci a bai wa Emefiele masauki a gidan yarin Kuje

An yi sallah don neman albashi a Zamfara

A wani labarin, wasu ma'aikatan gwamnatin jihar Zamfara sun gudanar da Salloli na musamman, a masallacin idin Gusau, babban birnin jihar ranar Asabar.

Jaridar Daily Trust ta kawo rahoto cewa ma'aikatan sun taru a masallacin idin ne da misalin karfe 10 na safe, inda suka nemi Allah ya kawo mu su dauki kan kudaden albashinsu.

Ma'aikatan sun bayyana cewa, rabon da a ba su albashi tun watan Janairu, wanda hakan ya jefa su cikin halin kakanikayi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.