Kungiyar NLC Ta yi Fada da Ministan Tinubu, Sun Ki Yarda Ayi Zama da Shi a Taro

Kungiyar NLC Ta yi Fada da Ministan Tinubu, Sun Ki Yarda Ayi Zama da Shi a Taro

  • Kwamred Joe Ajaero ya nesanta kungiyarsa ta NLC da Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Simon Lalong
  • Shugaban NLC na kasar ya fadi abin da ya jawo sabanin ‘yan kwadago da Ministan yayin da ake neman mafita
  • Ajaero ya ce an sabawa alkawarin da aka yi da Ministan wajen kawo karshen rigimar da ake yi a kungiyar NURTWA

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya yi shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja - Kungiyar NLC ta ‘yan kwadago ta yi barazanar gujewa taronta na yau da gwamnatin tarayya a kan batun yajin-aikinsu.

This Day ta ce shugabannin ma’aikatan Najeriyan sun ce ba za su zauna a kujera daya da Ministan kwadago, Hon. Simon Lalong ba.

Da yake magana da manema labarai jiya a Abuja, shugaban NLC na kasa, Kwamred Joe Ajaero ya ce an gayyace su taro a Aso Rock.

Kara karanta wannan

Ya kamata CBN ta sa a daina amfani sabbin takardun Naira da Buhari ya kawo, malami ya fadi dalilai

Kungiyar NLC
Femi Gbajabiamila ya kira NLC zuwa taro Hoto: @femigbaja
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin tarayya ta kira 'Yan NLC

Joe Ajaero yake cewa Rt. Hon. Femi Gbajabiamila ya kira su domin duba rahoton inda aka kwana wajen dabbaka alkawuran da aka yi.

Gwamnatin tarayya ta cin ma yarjejeniya da ‘yan kwadago bayan cire tallafin fetur.

Ajaero ya fadawa manema labarai cewa dalilin zaman na yau shi ne su duba su gani ko gwamnati ta cika alkawuran da ta daukan masu.

NLC ta yi bayanin abin da ya sa ba za ta shiga taron da Simon Lalong zai halarta ba.

Ajaero: Rigimar NLC da Simon Lalong

"Idan za ayi taron, dole ya zama babu Ministan kwadago da samar da ayyuka, ba za mu shiga taron da Ministan kwadago zai zauna ba.
Idan za ku tuna matsayarmu da mu ka dauka da kungiyar NURTW ita ce duka bangarorin rikicin su bar harabar saboda zaman lafiya.

Kara karanta wannan

Za a Biya Nnamdi Kanu Naira Biliyan 8 Bayan Kotu Ta Soke Haramcin Kungiyar IPOB

Amma har yanzu ba ayi hakan ba. Saboda haka taron da za mu yi da gwamnatin tarayya, Ministan kwadago ba zai shiga ciki ba."

Baya ga haka, NLC ta dauki alwashin cigaba da zanga-zangarta a birnin Owerri na jihar Imo a dalilin sabaninta da Gwamnatin jihar.

IPOB ta yi galaba a kan Gwamnati

Ana da labari Nnamdi Kanu zai tashi da N8bn daga hannun Gwamnatin Tarayya tun da IPOB ta yi galaba a Kotu a kan ta'addantar da kungiyar.

Kotun da ke zama a Enugu ta share takunkumin da aka kakabawa ‘Yan kungiyar IPOB saboda haka aka ce daure Nnamdi Kanu ya saba doka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Online view pixel