Gwamnatin Legas Ta Rufe Masallaci, Coci-Coci da Wuraren Tarurruka Kan Damun Jama’a

Gwamnatin Legas Ta Rufe Masallaci, Coci-Coci da Wuraren Tarurruka Kan Damun Jama’a

  • Gwamnatin jihar Legas ta sanar da rufe wasu coci-coci da masallaci a wasu yankuna da ke jihar saboda shiga hakkin mutane
  • Hukumar Kula da Muhalli ta jihar, LASEPA ita ta gudanar da wannan gagarumin aiki saboda yawan korafi da ake yi na damun jama’a
  • Kwamishinan Ma’aikatar Muhalli da Albarkatun Ruwa, Tokunbo Wahab shi ya tabbatar da haka a shafinsa na Twitter

Jihar Legas – Gwamnatin jihar Legas ta rufe wasu coci-coci da masallaci da kuma wuraren tarurruka a jihar saboda damun mutane da kara.

Hukumar Kula da Muhalli ta jihar (LASEPA) ita ta rufe wuraren ibadar da kuma wuraren tarurruka saboda shiga hakkin jama’a da su ke yi da kararraki.

Gwamnatin Legas ta rufe masallaci da coci-coci kan yawan damun jama'a
Gwamnatin Legas Ta Dauki Mataki Kan Masallaci da Coci-Coci. Hoto: Sanwo-Olu Babajide.
Asali: Facebook

Wane mataki Legas ta dauka kan masallaci da coci?

Kwamishinan Ma’aikatar Muhalli da Albarkatun Ruwa a jihar, Tokunbo Wahab shi ya tabbatar da haka a shafinsa na Twitter a yau Asabar 21 ga watan Oktoba, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

Mista Ibu: Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki Ya Dauki Nauyin Asibitin Jarumin Da Ke Jinya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wahab ya ce babban manajan hukumar, Tunde Ajayi shi ya jagoranci wannan aiki kan wuraren ibada da tarurruka saboda shiga hakkin jama’a da kuma kawo cikas ga muhalli.

Daga cikin wuraren da abin ya shafa akwai masallacin Ansar-Ud-deen da Cocin Restoration Global Centre, cewar Vanguard.

Sauran sun hada da wurin taro na Bloomberg da Club Hexagon da wurin shakatawa na Starrex da ke Agbada sai kuma Bayrock a Lekki Phase 1.

Wane martani mutane ke yi kan rufe masallacin da coci?

Wannan na zuwa ne yayin da mutane ke korafin cewa ana shiga hakkinsu da sautuka yayin da su ke cikin hutawarsu a cikin gidajensu.

Hukumar ta dauki wannan mataki ne don tabbatar da bai wa wadanda ake zalunta hakkinsu na ‘yan kasa

Sai dai mutane da dama sun yi korafi inda su ke cewa babu wani masallaci da aka kulle kawai iya coci-coci da wuraren tarurruka aka rufe.

Kara karanta wannan

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Shugaban Karamar Hukuma da Wasu Mutane 12 a Jihar Arewa

FCDA ta musanta rushe bangaren Masallacin Abuja

A wani labarin, ana zargin Hukumar Gudanarwa a Abuja, FCDA na shirin rushe wani bangare na babban masallacin Abuja.

Sai dai hukumar a cikin wata sanarwa da ta fitar ta musanta hakan inda ta ce babu kamshin gaskiya a ciki.

Daga bisani kwamitin masallacin shi ma ya fitar da sanarwa inda musanta rade-radin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.