Shugaba Tinubu Ya Kaddamar da Tallafin Kudi Ga Gidaje Miliyan 15

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar da Tallafin Kudi Ga Gidaje Miliyan 15

  • Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da shirin rabon tallafin kuɗi ga gidaje miliyan 15 domin rage musu raɗaɗi
  • Sabon shirin rabon tallafin kuɗaɗen dai zai amfani ƴan Najeriya miliyan 62 waɗanda ke fama da matsanancin talauci
  • Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume shi ne ya wakilci Shugaba Tinubu wajen ƙaddamar da shirin da aka yi a ranar Talata, 17 ga watan Oktoba

FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da shirin rabon tallafin kuɗi ga gidaje miliyan 15.

Jaridar Channels tv ta kawo rahoto cewa taron ƙaddamar da shirin ya gudana ne a ɗakin taro na ƴan jarida na gidan gwamnati da ke Abuja, a ranar Talata, 17 ga watan Oktoban 2023.

Shugaba Tinubu ya kaddamar da tallafin rabon kudi
Shugaba Tinubu ya kaddamar da tallafin rabon kudi ga gidaje miliyan 15 Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, shi ne ya wakilci Shugaba Tinubu a wajen taron wanda ya zo daidai da ranar yaƙi da fatara ta duniya.

Kara karanta wannan

Gwammatin Tinubu Ta Buɗe Shafin Ɗaukar Mutane Aikin N-Power Na 2023? Gaskiya Ta Bayyana

Tinubu ya sanar da shirin bayar da tallafin kuɗin ne a lokacin da ya gabatar da jawabin ranar samun ƴancin kai ga ƴan Najeriya a ranar 1 ga Oktoban 2023.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƴan Najeriya nawa ne za su amfana?

Ministar agaji da kawar da talauci, Betta Edu, ta ce gidaje miliyan 15 ɗin suna wakiltar ƴan Najeriya miliyan 62.

A cewar Edu, Naira 25,000 za a riƙa ba wadanda suka amfana da shirin a kowane wata har na tsawon watanni uku, rahoton Vanguard ya tabbatar.

Ministan ta ƙara da cewa za a kaddamar da wani sabon shiri mai suna ‘Iya Loja Funds’ domin bayar da lamuni mai sauƙi na N50,000 domin tallafa wa ƙananan ƴan kasuwa.

A wajen rabon kuɗin ga waɗanda za su amfana da shirin, ministan kuɗi, Wale Edun, ya bayyana cewa za a samar da tsarin tantance wa na amfani da bayana ƴan yatsu domin tabbatar da gaskiya da bin diddigi.

Sabon Tallafin Tinubu Ga Dalibai

A wani labarin kuma, shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sabon tallafi ga ɗaliban Najeriya da ke karatu a makarantun gaba da sakandare.

Shugaban ƙasar ya bada umarnin raba motocin Bas-Bas ga jami'o'i, kwalejojin fasa da kwalin ilimin da ke sassan ƙasar nan baki ɗaya, domin sauƙaƙawa ɗalibai wajen zirga-zirga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng