Ministoci: Na Hannun Daman Atiku Ya Ambaci Kuskure Bayan Tinubu Ya Rabawa Ministoci Ma'aikatu

Ministoci: Na Hannun Daman Atiku Ya Ambaci Kuskure Bayan Tinubu Ya Rabawa Ministoci Ma'aikatu

  • Jigo a jami'iyyar PDP, Barista Daniel Bwala ya soki rarraba ma'aikatu na ministocin Tinubu
  • Bwala ya kasance na hannun daman dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar
  • Ya ce ta yaya za a dauki ma'aikatar tsaro a ba wa Bello Matawalle da ya gagara kawo karshen rashin tsaro a jihar Zamfara

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT, Abuja - Barista Daniel Bwacha na hannun daman dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP ya magantu kan ministocin Shugaba Tinubu.

A ranar Laraba 16 ga watan Agusta, Tinubu ya ba wa sabbin ministoci ma'aikatu wadanda majalisar Dattawa ta tantance, Legit.ng ta tattaro.

Barista Bwala ya soki tsarin yadda Shugaba Tinubu ya rarraba ma'aikatu ga ministoci
Bwala Ya Bayyana Kuskure A Ma'aikatun Da Aka Rabawa Ministoci. Hoto: Bwala Daniel, Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Meye Bwala ya ce kan mukaman ministoci?

Barista Bwala ya ce a mukaman akwai wadanda ba su dace da ma'aikatun da aka ba su ba ko kadan.

Kara karanta wannan

Wahalar da Ake Sha Tamkar Nakuda ce, Bola Tinubu Ya Ce Za a Haifi Jariri

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ya ce dukkan ministocin ba su da alaka kuma ba su dace da mukamin ba ganin yadda Tinubu ya rarraba su.

Ya ce:

"Akwai ministoci kwararru amma ma'aikatun da aka ba su ba su dace da su ba."

Bwala ya ba da misalin Hannatu Musawa da aka ba wa ministar al'adu madadin ma'aikatar jin kai, Vanguard ta ruwaito.

Shin Matawalle ya dace da ministan tsaro?

Hannatu ta fito daga jihar Katsina da ke yankin da ya ke bukatar jin kai ga mutane saboda matsalolin tsaro.

Jigon PDP ya kuma koka kan yadda Bola Tinubu ya damkawa Bello Matawalle karamin ministan tsaro.

Bwala ya ce ta yaya mutumin da ya gagara dakile matsalar tsaro a jihar Zamfara zai yi kokari a tsaron kasa baki daya.

Kara karanta wannan

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Raddi Kan Zargin Zaluntar ‘Yan Arewa a Rabon Mukaman Minista

Ya ce ma'aikatar tsaro na taka muhimmiyar rawa wurin tabbatar da kare kasa daga hare-hare da kuma zaman lafiyar al'umma.

Tinubu Ya Raba Mukaman Ministoci

A wani labarin, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya sanar da ma'aikatun ministoci 45 da aka kammala tantancewa a majalisar Dattawa a kwanakin baya.

Daga cikin ministoci 48, an tabbatar da 45 yayin da guda uku ke jiran sakamakon bincike da ake yi a kansu.

Daga cikin wadanda su ka samu mukaman akwai Nyesom Wike, ministan Abuja sai Badaru Abubakar, ministan tsaro da kuma Bello Matawalle karamin ministan tsaro.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.