Masu Ruwa Da Tsaki A APC Sun Roki Tinubu Ya Sauya El-Rufai Daga Kudancin Kaduna

Masu Ruwa Da Tsaki A APC Sun Roki Tinubu Ya Sauya El-Rufai Daga Kudancin Kaduna

  • Kungiyar masu ruwa da tsaki a jam'iyyar APC ta jihar Kaduna ta roki Tinubu kan na da minista daga Kudancin Kaduna
  • Ta ce ganin yadda Nasir El-Rufai ya ajiye mukamin minista, zai fi kyau a duba bangaren Kaduna ta Kudu a yanzu
  • Ibrahim Koli, shugaban APC na karamar hukumar Jema'a a jihar shi ya bayyana haka a madadin kungiyar a cikin wata sanarwa

FCT, Abuja - Masu ruwa da tsaki a jam'iyyar APC mai mulki a jihar Kaduna sun bukaci Shugaba Tinubu ya zabo minista daga Kudancin Kaduna.

Wannan na dauke ne a cikin wata sanarwa da shugaban jam'iyyar APC na karamar hukumar Jema'a, Ibrahim Koli ya sanya wa hannu.

APC ta bukaci Tinubu ya maye gurbin El-Rufai daga Kaduna ta Kudu
Jam'iyyar APC Ta Roki Tinubu Ya Sauya El-Rufai Daga Kaduna Ta Kudu. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

Me APC ta ce kan mukamin El-Rufai?

Ya ce bisa ga alamun cire sunan Nasir El-Rufai, ya fi kyau a dauko madadin shi daga Kudancin Kaduna don samun daidaito.

Kara karanta wannan

DSS: ‘Yan Ta’adda Sun Yi Shirin Kai wa Mutane Mugun Hari a Jirgin Abuja-Kaduna

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya ce:

"Wannan kungiya da ta kunshi tsoffin shugabannin kananan hukumomi da masu ci da kuma manyan masu mukami a APC muna kira ga Tinubu da ya dauko minista daga Kudancin Kaduna.
"Ganin yadda tsohon gwamnan jihar, Nasiru El-Rufai ya ajiye neman kujerar minista da kansa, zai fi kyau a dauko madadinshi daga wannan yanki.
"Abin takaici ne yadda kowa ya goyi bayan El-Rufai a kan kujerar ministan, amma kuma yanzu ya ki amincewa da tayin."

Koli ya ce a Kudancin Kaduna su na da mutane jajirtattu da za su rike wannan kujera ta minista, cewar Vanguard.

Da waye su ke son a maye El-Rufai?

Koli ya ce:

"Mu na roko a sake ba mu dama a Kudancin Kaduna wanda mu ka rasa tun hawan gwamnatin APC a 2015.
"Mu na da jajirtattu kamar Dakta Abdulmalik Dogonruwa wanda shi ne kwamishinan Tarayya na hukumar kidaya.
"Dogonruwa na da kwarewa matuka a fannin aiki da kuma irin gudumawa da ya bayar a zaben 2023 da ya gabata a Kudancin Kaduna."

Kara karanta wannan

Shari'ar Gwamnan Kano: Mataimakin Shugaban Majalisa Ya Roki Yan Najeriya Su Taya APC Addu'ar Samun Nasara Kan PDP

Ibrahim ya ba wa shugaban kasa, Bola Tinubu tabbacin cewa ba zai yi dana sanin na da Dogonruwa minista ba, cewar Leadership.

El-Rufai Ya Hakura Da Mukamin Minista

A wani labarin, Malam Nasiru El-Rufai ya ce ba ya sha'awar zama minista a gwamnatin Tinubu.

El-Rufai ya ajiye mukamin ne bayan cikas da aka samu yayin tantance shi a majalisa inda ya ce yana da wanda zai maye gurbinshi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.