Jerin Ministocin Kudi A Najeriya Tun Daga 1999 Zuwa Yanzu Da Kuma Jihohinsu

Jerin Ministocin Kudi A Najeriya Tun Daga 1999 Zuwa Yanzu Da Kuma Jihohinsu

‘Yan Najeriya sun zaku su san waye zai karbi ma’aikatar kudi a matsayin minista saboda tasirin ma’aikatar da kuma yadda tattalin arzikin kasar ke tangal-tangal

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Matsayin ministan kudi a Najeriya na da matukar girma da kuma daraja wanda mutane ke mutuntawa saboda tasirin kudade a kasar.

Tun shekarar 1999, gwamnati ta nada ministocin kudi guda takwas da suka hada da Adamu Ciroma da Olusegun Aganga da kuma Ngozi Okonjo-Iweala, Legit.ng ta tattaro.

Jerin minitocin kudi da aka yi a Najeriya tun 1999 zuwa 2023
Jerin Ministocin Kudi a Najeriya Tun Daga 1999 Zuwa Yanzu. Hoto: Kimihiro Hoshino/Shawn Thew.
Asali: Getty Images

Legit.ng Hausa ta tattaro muku jerin ministocin kudi tun 1999 bayan dawowar dimukradiyya a Najeriya.

1. Adamu Ciroma (1999-2003) – Jihar Yobe

Ciroma shi ne gwamnan babban bankin Najeriya, CBN a gwamnatin Murtala Mohammed kafin zama minista a 1999.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Tashin Dala: Daliban da Najeriya ta Aika Karatu na Ganin Tashin Hankali a Kasar Waje

Ya kasance a fannin tattalin arziki duk da cewa masanin tarihi ne, daga bisani ya kasance minsitan kamfanoni da kasuwanci.

Ya nemi takarar shugaban kasa har sau biyu a rayuwarsa kafin ya rasu a ranar 5 ga watan Yuli 2018 ya na da shekaru 83.

2. Ngozi Okonjo-Iweala (2003-2006) – Jihar Delta

Ngozi ta kasance masaniyar tattalin arziki da ake tunanin babu kamarta a Nahiyar Afirka gaba daya.

An haife ta a ranar 13 ga watan Yuni a 1954 a Ogwashi-Ukwu da ke jihar Delta, Ngozi ta kasance ministar kudi a gwamnatoci biyu (2003-2006) da kuma (2011-2015).

3. Nenadi Usman (2006-2007) – Jihar Kaduna

Nenadi Esther Usman an haife ta a ranar 12 ga watan Nuwamba 1966 a karamar hukumar Jere da ke jihar Borno, Usman ba ta jima ba a kan kujerar ministan kudi.

An zabe ta a matsayin Sanata daga Kaduna ta Kudu a watan Afrilu na 2011 a tutar jam’iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Muddin Aka Sake Kara Farashin Fetur, Za Mu Birkita Kasar Nan da Yajin Aiki Inji NLC

4. Shamsudden Usman (2007-2009) – Jihar Kano

Usman ya fara karatunsa ne a King’s College da ke Legas inda daga baya ya wuce jami’ar Ahmadu Bello da ke Zari’a jihar Kaduna a fannin tsangayar tattalin arziki.

Shamsudden ya yi aiki a bankuna da dama kafin kasancewarshi ministan kudi a gwamnatin marigayi Umaru Musa Yar’adua.

5. Mansur Mukhtar (2009-2010) – Jihar Borno

Mansur shi ma ya kasance dalibi daga King’s College kafin daga bisani ya wuce jami’ar Ahmadu Bello da ke Zari’a.

Kafin kasancewarshi ministan kudi a gwamnatin marigayi ‘yar Adu’a ya yi aiki a bankuna da dama da sauran hukumomin kudi a Najeriya.

6. Olusegun Aganga (2010-2011) – Jihar Ekiti

An haifi Aganga a ranar 22 ga watan Yuli na 1955, ya kasance masanin tattalin arziki da ya shahara a Najeriya.

A lokacin da ya ke ministan kudi shi ya kawo tsarin fadada tattalin arziki inda kasar ta rage dogaro da man fetur a kasar.

Kara karanta wannan

Tarihin Duka Juyin Mulkin Da Aka Taba Yi Daga 1974 Zuwa 2023 a Jamhuriyyar Nijar

7. Ngozi Okonjo-Iweala (2011-2015) – Jihar Delta

Kasancewarta masaniyar tattalin arziki da kuma kwarewarta shi ya sake bata damar dawowa a matsayin ministar kudin lokacin mulkin Goodluck Ebele Jonathan.

Bayan gwamnatinsu ta kare, an nada Ngozi a matsayin Babbar Darakta a Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO) a 2021.

8. Kemi Adeosun (2015-2018) – Jihar Ogun

Adeosun ta rike kujerar minista na shekaru uku kacal bayan cece-kuce a kan takardar shaidar bautar kasa wato NYSC.

A watan Satumba na 2018, Adeosun ta ajiye mukamin ministar kudi saboda cece-kuce da ake ta yi a kan haka.

9. Zainab Ahmed (2018-2023) – Jihar Kaduna

An haifi Zainab a ranar 16 ga watan Yuni na 1960, ta samu shaidar kammala digiri a jami’ar Ahmadu Bello yayin da ta sake yin digiri na biyu a jami’ar jihar Ogun inda ta karanta harkar kasuwanci.

A lokacin da ta ke rike da mukamin ministar kudi, Ahmed ta ba da gudumawa sosai wurin ganin an samu karuwar tattalin arziki a kasar.

Kara karanta wannan

Kyau Ya Hadu Da Kyau: Diyar Biloniya Indimi Ta Amarce Da Babban Dan Kasuwar Kasar Turkiyya

Akwai Yiwuwar Ministan Kudi Ya Fito Daga Legas

A wani labarin, ana hasashen shugaban kasa, Bola Tinubu zai iya dauko ministan kudi daga jihar Legas.

Wani babban lauya da ke zaune a Legas, Wale Adeagbo shi ya bayyana haka yayin hira da Legit.ng ta yi da shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.