Kada Ku Tsoma Baki Tare da Haifar Mana Matsala, Babban Malamin Coci Primate Ya Caccaki Kasashen Turai

Kada Ku Tsoma Baki Tare da Haifar Mana Matsala, Babban Malamin Coci Primate Ya Caccaki Kasashen Turai

  • Jagororin juyin mulkin a Jamhuriyar Nijar suna ci gaba da ja bukatur kasashen duniya na barin shugaba Mohamed Bazoum ya dawo kan karagar mulkinsa
  • Rashin samun hadin kan wadanda suka yi juyin mulkin ya sa Faransa ka yi Allah wadai da su; A da Nijar ta kasance cikin kasashen yammacin Afirka da Faransa ke da alaka da su
  • Da yake magana kamar yadda jama’a da dama suka yi kan Nijar, limamin coci Primate Elijah Ayodele ya shawarci kasashen yammacin duniya da su bi a hankali

Yamai, Jamhuriyar Nijar - Primate Elijah Babatunde Ayodele, shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual da ke Legas a Najeriya, ya bukaci kasashen yammacin duniya da su guji dama lamurra a Jamhuriyar Nijar da aka yi wa juyin mulki kwanan nan.

A cewar Primate Ayodele, "hakan zai kai ga kashe talakawa da hambararren shugaban kasar, Mohamed Bazoum".

Kara karanta wannan

Ya ake ciki? An fadi yanayin da Bazoum ke ciki bayan ganawarsa da likitansa

Malami ya gargadi turawa kan yaki da Nijar
Malami ya caccaki Turawa kan ingiza 'yan Afrika | Hoto: AFP
Asali: Getty Images

‘Kada a zubar da jini a Nijar': Primate Ayodele

An bayyana batun Primate Ayodele ne a wani faifan bidiyo da aka uada a shafinsa na Twitter a ranar Lahadi, 13 ga watan Agusta.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A kalamansa:

“Kada ku gwada wata matsala a Nijar. Zubar da digon jini zai kai ga rasa ran shugaban kasar.
"Ya kamata mu warware matsalar Nijar cikin lumana da kwanciyar hankali domin kowa zai nake hannu ya bar jama'a su yi duk abin da suke so."

Matsalar da za ta faru idan aka matsa lamba

Ya ci gaba da cewa:

“Lokacin da kuke shirin haifar da matsaloli ko dama lamura, da gaske za ku haifar da barazana ga rayuwar shugaban kasa.
“Juyin mulkin Nijar ba zai kau ba, kuma duk wanda ke kokarin kawo karfin soja zai haifar da abubuwa da yawa. Kada su kyale irin wannan ya faru.

Kara karanta wannan

Daga karshe: Malaman Izala sun dira Nijar don neman hanyar sulhu a batun juyin mulki

"Ya kamata mu dauki lamarin cikin sauki kuma mu yi taka-tsan-tsan ta yadda lamarin ba zai kai ga abin da ba mu zata ba."

Izala ta kai ziyarar sulhu Nijar

Fitattun malaman addinin Musulunci karkashin jagorancin shugaban kungiyar Izala ta kasa Sheikh Bala Lau, sun dira jamhuriyar Nijar a wani mataki na neman hanyar da za ta sa a sasanta lamarin da ya faru na juyin mulki.

A hotunan da Legit.ng Hausa ta gani a shafin Twitter na kafar Zagazola Makama, an ga lokacin da malaman suka sauka a Nijar.

An gano malaman a filin jirgin sama, inda suka samu tarba daga jami’an sojin jamhuriyar ta Nijar da ke makwabataka da Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.