Ku Ayyana Ni a Matsayin Shugaban Kasan Najeriya, Atiku Ya Fadawa Kotu a Jawabinsa Na Karshe

Ku Ayyana Ni a Matsayin Shugaban Kasan Najeriya, Atiku Ya Fadawa Kotu a Jawabinsa Na Karshe

  • Da alamu shugaban kasa Tinubu zai fuskanci damuwa kan shari’arsa da dan takarar shugaban kasa na PDP
  • Ya zuwa yanzu, Atiu ya nemi a alanta shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa a Najeriya
  • Atiku ya kafa hujjojin da ya ce shi ne ya lashe zaben, kana kotu bata musanta cewa shi ne ya ci zabe a jihohi 21 ba

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT, Abuja - Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Abubakar Atiku, ya bukaci kotun sauraran kararrakin zabe da ta tabbatar da sanarwar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi cewa shi ne ya lashe jihohi 21 a zaben shugaban kasa da aka gudanar a bana.

Atiku ya yi wannan batu ne a ranar Juma’a a jawabinsa na karshe na kare kokensa na hadin gwiwa da jam’iyyar PDP na neman a soke alanta Ahmed Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa, rahoton Daily Post.

Kara karanta wannan

PDP Ta Yi Hasashen Abun Da Zai Faru Idan Kotu Ta Tsige Shugaba Tinubu

Atiku ya nemi kotu ta tsige Tinubu ta ba shi kujerar mulki
Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasan PDP | Hoto: vanguardngr.com
Asali: UGC

A jawabin karshe da babban lauyansa Chris Uche SAN ya yi, Atiku ya bayyana cewa INEC ta ce shi ya ci zabe a jihohi 21, ba a yi jayayya ba, ko janye batun, ko ma karyata shi, ko kuma da’awar cewa kuskure ne a tsawon shari’ar kotun zuwa yanzu.

Martanin hukumar zabe ta INEC

INEC ta mayar da martani ga karar Atiku, inda ta ce dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP ya lashe jihohi 21 na tarayyar kasar a zaben shugaban kasa da ya gabata, Channels Tv ta ruwaito.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Jihohin 21 da INEC ta bayyana cewa Atiku da PDP sun lashe sun hada da Adamawa, Akwa Ibom Bauchi, Bayelsa, Borno, Delta, Ekiti, Gombe, Jigawa, Kaduna, Katsina, Kebbi, Kogi, Kwara, Nasarawa, Niger, Osun, Sokoto, Taraba, Yobe da Zamfara.

Kara karanta wannan

Bayanai Sun Fito: An Bayyana Wanda Shugaba Tinubu Ya Ke Son Nada Wa Minista Daga Jihar Ogun

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce tun da hukumar zaben ta yi ikirarin cewa shi ne ya lashe wadannan jihohin kuma ya yi fatali da hakan a duk zaman da ake a shari’ar, ya kamata kotun ta tabbatar da shi ne shugaban kasa.

Kotu ta amince da korafin Atiku kan Tinubu dangane da Jami'ar Chicago da shaidar yin NYSC

A wani labarin, kotun sauraran korafe-korafen zabe a Abuja ta amince da shaidar da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya gabatar.

Kotun ta karbi wannan takardun ne a ranar Juma'a 23 ga watan Yuni da suka hada da takardar shaidar bautar kasa da na kammala digiri da kuma takardar shaidar aiki na kamfanin Mobil Oil Nigeria Plc.

Jam'iyyar PDP ta gabatar da shaidar ta hannun Mike Enahoro Ebah wanda ya ce takardun Tinubu ne ya karbe su amma suna dauke da sunan Bola Adekunle Tinubu, Daily Trust ta tattaro.

Kara karanta wannan

Yanzu nan: Shugaban APC Ya Hakura da Rikon Jam’iyya, Ya Sauka Daga Kujerarsa

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Online view pixel