Gwamna Da Kan Shi Ya Jawo Jama'a Zuwa Sallar Ruwa Saboda Yankewar Damina

Gwamna Da Kan Shi Ya Jawo Jama'a Zuwa Sallar Ruwa Saboda Yankewar Damina

  • Gwamna Bala Abdulqadir Mohammed ya tura wakilci wajen sallar rokon ruwa da aka shirya a jiya
  • Auwal Jatau ya wakilci gwamnan a wajen ibadan matsayin na mataimakin gwamnan jihar Bauchi
  • Dinbin mutane sun halarci sallar da Na’ibin limamin garin Bauchi, Ahmad Inuwa-Na’ibi ya jagoranta

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Bauchi - Gwamna Bala Abdulqadir Mohammed na jihar Bauchi, ya jagoranci mutane a wurin sallar rokon ruwa a ranar Alhamis.

Daily Trust ta tabbatar da cewa Mai girma Gwamnan Jihar Bauchi yana cikin wadanda su ka bi wannan sallah ta musamman.

Da yake jawabi bayan an idar da sallar, Bala Abdulqadir Mohammed ya ce sun dade su na sa ran ruwan sama a har yanzu bai sauko ba.

Gwamna
Gwamnan Bauchi, Senator Bala A. Mohammed Hoto: @SenBalaMohammed
Asali: Twitter

Jama'a sun komawa Allah (SWT)

Ganin halin da aka shiga, Gwamnan ya ce al’ummar jihar Bauchi su ka dukufa wajen rokon Allah (SWT) domin ya sauko da ni’imarsa.

Kara karanta wannan

Tinubu Ya Bukaci Majalisa ta nada Mutanen da Buhari Ya Ki Amincewa da su a Gwamnati

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Gwamna Bala Mohammed ya yi kira ga mutane su cigaba da addu’o’i domin manoman Bauchi su ci moriyar daminar shekarar bana.

Auwal Jatau ya wakilci Gwamna

The Nation ta ce Mataimakin Gwamna, Auwal Jatau ya wakilci Gwamnan a wajen sallar.

Auwal Jatau ya yabawa Mai martaba Sarkin Bachi, Rilwanu Adamu da sauran malaman addinin musulunci da su ka shirya sallar rokon.

A jawabinsa, Jatau ya ce gwamnatinsu ta kawo tsare-tsare da su kawo cigaba tun daga saida taki da araha zuwa samar da tsaro a noma.

Na’ibin limamin garin Bauchi, Ahmad Inuwa-Na’ibi ya jagoranci sallar, Sakataren gwamnati, Ibrahim Kashim da daruruwa sun halarta.

Ana kuka a wasu garuruwa

Legit.ng Hausa ta fahimci an fara kiran a yi irin wadannan salloli a garin Kano. A Borno kuwa sai da Shehu ya jagoranci sallar rokon ruwa.

Kara karanta wannan

An Damke Sarkin Arewa da Mai Dakinsa a Kudancin Najeriya Saboda Alaka da Emefiele

Zanna Bukar Guzamala mutumin Borno ne, ya fadawa Legit.ng Hausa tun bayan sallah, sau daya aka yi ruwa, kayan gona suna ta lalacewa."

"Ruwa ya tsaya tun bayan sallah, amma da Shehu Borno ya jagoranci sallah, an samu ruwa a was wurare a jiya (ranar Alhamis).
Shehu ya umarci Hakimai su cigaba da yin wannan roko a kasashensu. Kuma ko ina su na yi.”

- Zanna Bukar Guzamala

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Online view pixel