Jerin Sunayen Sabbin Kwamishinonin Yan Sanda da Aka Tura Jihohi 8

Jerin Sunayen Sabbin Kwamishinonin Yan Sanda da Aka Tura Jihohi 8

  • Hukumar jin daɗin 'yan sanda ta ƙasa ta amince da tura sabbin kwamishinonin 'yan sanda zuwa jihohi 8 a Najeriya
  • Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da jami'in hulɗa da jama'a na hukumar PSC, Ikechukwu Ani, ya fitar ranar Jumu'a, 30 ga watan Yuni, 2023
  • Sanarwan ya bayyana jihohin da suka samu sabbin kwamishinonin, wanda ya haɗa da Borno, Kebbi, Imo, Anambra, Oyo, Ebonyi, Kwara da Ogun

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT Abuja - Hukumar jin daɗin 'yan sandan Najeriya (PSC) ta amince da tura sabbin kwamishinoni zuwa rassan hukumar 'yan sanda a jihohi takwas, kamar yadda jaridar The Cable ta ruwaito.

Jami'in hulɗa da jama'a na hukumar PSC, Ikechukwu Ani, shi ne ya bayyana tura sabbin kwamishinonin a wata sanarwa da ya fitar ranar Jumu'a, 30 ga watan Yuni, 2023.

Kara karanta wannan

Wane Hukunci Aka Ɗauka Kan Kwamishinan Zaben Adamawa Hudu Ari? INEC Ta Fallasa Gaskiya

Sabbin kwamishinonin 'yan sanda 8.
Jerin Sunayen Sabbin Kwamishinonin Yan Sanda da Aka Tura Jihohi 8 Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Legit.ng Hausa ta tattaro muku cewa jihohin da suka samu sabbin kwamishinonin 'jami'an 'yan sanda sun ƙunshi, Borno, Kwara, Oyo, Kebbi, Ebonyi, Ogun, Anambra, da kuma Imo.

Hukumar ta yaba wa sabon mukaddashin sifetan 'yan sanda na ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, bisa natsuwa da kiyaye jinsi wajen tura waɗanda suka dace da muƙaman, This Day ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban hukumar jin daɗin 'yan sanda na ƙasa, Solomon Arase, ya buƙaci sabon muƙaddashin IGP ya riƙa la'akari da illar shiyyoyin ƙasar nan yayin tura sunayen waɗan da ya dace ga PSC.

Jerin sunayen sabbin kwamishinonin 'yan sanda da kuma jihohin da za su jagoranta

Mun haɗa muku jerin sunayen sabbin kwamishinonin jami'an yan sanda da kuma jihohin da zasu jagoranta, ga su kamar haka:

1. Godwin Aghaulor - jihar Borno

2. Adelesi E. Oluwarotimi - jihar Kwara

Kara karanta wannan

Babbar Sallah: "Ku Ji Tsoron Allah" Manyan Malamai Sun Aike da Muhimmin Saƙo Ga Sabbin Shugabanni

3. Adebola Ayinde Hamzat - jihar Oyo

4. Augustina Ogbodo - jihar Ebonyi

5. Samuel Titus Musa - jihar Kebbi

6. Aderemi Adeoye - jihar Anambra

7. Stephen Olarewaju - jihar Imo

8. Alamatu Abiodun - jihar Ogun.

Falana Ya Bukaci DSS Ta Hanzarta Bincike, Ta Gurfanar da Bawa da Emefiele a Kotu

A wani labarin na daban mun kawo muku cewa Femi Falana, babban lauya mai fafutukar kare hakkin ɗan adam ya buƙaci DSS ta gaggauta kammala bincike kan Bawa da Emefiele.

Falana ya roƙi hukumar DSS ta gurfanar da mutanen biyu idan ta gano cewa suna da hannu a tuhume-tuhumen da ake masu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262