Kaduna: Uba Sani Ya Nada Tsohon Kwamishinan El-Rufai Shugaban KCTA

Kaduna: Uba Sani Ya Nada Tsohon Kwamishinan El-Rufai Shugaban KCTA

  • Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya nada tsohon kwamishinan Nasiru El-rufai, Samuel Aruwan a matsayin shugaban KCTA
  • Aruwan ya kasance tsohon kwamishinan tsaron cikin gida a tsohuwar gwamnatin Mallam Nasir El-rufai
  • Gwamnan ya yi nade-naden mukamai da dama tun farkon hawanshi karagar mulki inda ya nada mafi yawan yaran Nasir El-rufai

Jihar Kaduna - Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya nada tsohon kwamishinan Nasiru El-rufai, Samuel Aruwan a matsayin shugaban Hukumar Kula da Birnin Kaduna (KCTA).

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa sakataren yada labaran gwamnan, Muhammad Shehu a ranar Talata 20 ga watan Yuni.

Uba Sani ya nada Samuel Aruwan mukamin shugaban KCTA
Tsohon Kwamishinan El-Rufai, Samuel Aruwan. Hoto: Daily Nigerian.
Asali: Facebook

Aruwan shi ne tsohon kwamishinan tsaron cikin gida a gwamnatin El-Rufai

Mista Aruwan shi ne tsohon kwamishinan tsaron cikin gida a tsohuwar gwamnatin Nasiru Elrufai, Daily Nigerian ta tattaro.

Kara karanta wannan

An Ba Abba Gida-Gida Wa’adin Awanni 72 Ya Dakatar Da Rushe-Rushe a Kano, Cikakken Bayani

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar sanarwar:

"Aruwan ya kammala digiri a fannin aikin jarida, ya shafe shekaru a bangaren aikin jarida kafin ya dawo aikin gwamnati a 2015.
"Yana kuma da kwarewa ta fannin dakile tare da gudanar da matsalar tsaro ta yanda ya dace."

Aruwan ya ba da gudumawa sosai a bangarori da dama a jihar

Sanarwar ta kara da cewa kamar yadda Leadership ta tattaro:

"Bayan ba da gudunmawa ta fannin kawo zaman lafiya a jihar Kaduna.
"Ya kuma ba da gudumawa wajen wayar da kan jama'a a bangaren ta'addanci da kuma 'yan fashin daji a Arewacin Najeriya."

Da yake taya shi murnanr samun wannan matsayi, Gwamna Uba Sani ya roki Aruwan da ya yi amfani da kwarewar da ya ke da shi wurin kawo ci gaba a hukumar KCTA.

Ya yi masa fatan alkairi da samun wannan matsayi, inda ya yi addu'ar ubangiji ya taimake shi.

Kara karanta wannan

Abba Gida-Gida Ya Naɗa Kwamishinoni 19, Ya Tura Sunayensu Ga Majalisar Dokokin Kano

Uba Sani Ya Nada Mukarraban Tsohon Gwamna El-Rufai Manyan Mukamai

A wani labarin, gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya yi sabbin nade-nade a gwamnatinsa wanda ya hada da mukarraban tsohon gwamna.

Gwamnan ya nada mukarraban tsohon Gwamna Nasir El-Rufai manya-manyan mukamai a gwamnatinsa.

Sakataren yada labaran gwamnan, Muhammad Lawal Shehu shi ya sanar da nada wadannan mukamai, inda ya ce an duba kwarewa ce wajen nada mukaman.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.