Hukumar Zabe Zaman Kanta Ta INEC Ta Dage Zabe a Rumfunan Zabe 141

Hukumar Zabe Zaman Kanta Ta INEC Ta Dage Zabe a Rumfunan Zabe 141

  • Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta bayyana dage zabe a wasu rumfunar zabe 141 a jihar Omo
  • Wannan ya faru ne sakamakon tsaikon da aka samu a rumfanar na sace na'urorin tantance masu kada kuri'u na BVAS
  • An yi zabe a wasu bangarori daban-daban na Najeriya, ba a samu tsaiko ko tashin hankali ba

FCT, Abuja - Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta dage zabe a wasu rumfunan zabe 141 a jihar Imo da ke Kudancin Najeriya.

Wannan na fitowa ne daga bakin shugaban hukumar, Mahmud Yakubu a yau Asabar 25 ga watan Faburairu a birnin tarayya Abuja.

Dagewar ta shafi zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisun tarayya a yankunan, kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito.

An dage zabe a wasu rumfuna 141 a Najeriya
Mahmud Yakubu, shugaban hukumar zabe ta INEC | Hoto: dailypost.com
Asali: UGC

An kuma ruwaito cewa, shugaban INEC ya ce za a yi zaben a gobe Lahadi 26 ga watan Faburairu.

Kara karanta wannan

Sakamako: Tinubu ya lashe zabe a rumfarsa, an fadi kuri'unsa da na Atiku

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Meye ya faru?

Yakubu na magana ne game da abubuwan da aka lura dasu da kuma suka faru a zaben da aka gudanar a kasar.

Ya kuma bayyana cewa, an samu tsaiko yayin da wasu 'yan daba suka sace na'urorin tantance masu kada kuri'a ta BVAS a wasu yankunan Najeriya.

Hakazalika, ya ce 'yan sanda sun yi nasarar kwato wasu daga cikin na'urorin da 'yan daba suka sace, Punch ta ruwaito.

Ya kara da cewa:

"Ina farin cikin fadin cewa tsarin yana tafiya kuma za a bar 'yan Najeriya su yi zabensu a wuraren da lamarin ya faru."

Zaben 2023 da yadda ake ciki

A yau ne dai 'yan Najeriya suka fito domin zaban shugaban kasan da zai gaji Buhari da kuma 'yan majalisun tarayya 468 a zaben 2023.

Hakazalika, nan da mako biyu ne za a yi zaben gwamnoni da 'yan majalisun jihohi a ranar 11 ga watan Maris.

Kara karanta wannan

Karin bayani: 'Yan daba sun sace na'urar aikin zabe a jihar su Buhari da kuma wata jihar

Zaben bana shine zabe na bakwai da aka yi a Najeriya tun bayan da aka koma mulkin dimokradiyya a 1999.

A wasu rahotanni, kun ji yadda wasu 'yan daba suka sace na'urorin zabe a jihohin Katsina da Delta.

An kwato wasu daga cikin na'urorin, an kuma maye gurbin was don ci gaba da aikin zabe ba tare da wata matsala ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.