Kotun Koli Ta Kori Bwacha a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Taraba a Jam’iyyar APC

Kotun Koli Ta Kori Bwacha a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Taraba a Jam’iyyar APC

  • Kotun koli ta kori dan takarar gwamnan APC a jihar Taraba bisa gano dambarwa a zaben fidda gwanin da aka gudanar
  • Wannan na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta mai zama a Yola ta yi watsi da hukuncin korar dan takarar a baya
  • A baya, babbar kotun tarayya ta soke zaben fidda gwanin gwamnan APC da aka gudanar a jihar ta Taraba

FCT, Abuja - Kotun koli ya soke zaben Emmanuel Bwacha a matsayin dan takarar gwamnan jam’iyyar APC a jihar Taraba, TheCable ta ruwaito.

Da suke yanke hukunci a ranar Laraba, alkalai biyar na kotun koli karkashin jagorancin mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun sun tabbatar da hukuncin kotun tarayya na soke zaben fidda gwanin gwamnan Taraba na APC.

A watan Satumban bara, kotun tarayya a Jalingo ya soke zaben fidda gwanin gwaman APC da ya samar Bwacha a matsayin dan takarar APC.

Kara karanta wannan

Assha: Dan takarar majalisa a jam'iyyar su Kwankwaso a Arewa ya sace N681m daga asusun banki

Kotu ta kori Bwacha daga takarar gwamnan Taraba
Kotun Koli Ta Kori Bwacha a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Taraba a Jam’iyyar APC | Hoto: thecable.ng
Asali: UGC

Yadda batun shiga kotu ya faro

David Sabo Kente, daya daga cikin ‘yan takarar gwamnan APC ne ya maka Bwacha a kotu, inda ya kalubalanci sahihancin nasararsa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Simon Amobeda, alkalin kotun tarayya da ke zama a Jalingo ya amince da bukatar wanda ya shigar da kara cewa, ba a yi sahihin zaben fidda gwanin gwamna a Taraba ba.

Ya kuma yi Allah-wadai da fitar da sakamakon karya da baturen zabe ya yi a filin jirgi tare da cika wandonsa da iska zuwa kasar waje ta yi a a lokacin da aka yi zaben na fidda gwanin gwamna.

Alkalin ya umarci a sake sabon zaben fidda gwanin gwamnan APC a jihar cikin kwanaki 14, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Hukuncin baya-bayan nan

Sai dai, a ranar 24 ga watan Nuwamban bara, kotun daukaka kara a birnin Yola ya yi watsi da hukuncin babbar kotun da ta kori Bwacha.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Gwamnan CBN ya Dira Majalisar Tarayya, Ya Shiga Ganawa da Kakakin Majalisa

Amma duk da haka, Kente bai saduda ba, ta hannun lauyansa Kanu Agabi ya sake shigar da kara a gaban kotun koli.

A hukuncinta na yau, kotun koli kuwa ta kori Bwacha tare da rusa zaben, inda kotun yace an tafka kuskure a zaben na APC.

A halin da ake ciki dai, kotun koli ya yi watsi da batun kotun daukaka kara, ya tabbatar da hukuncin babbar kotun tarayya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.