Kotun Koli Ta Kori Bwacha a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Taraba a Jam’iyyar APC

Kotun Koli Ta Kori Bwacha a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Taraba a Jam’iyyar APC

  • Kotun koli ta kori dan takarar gwamnan APC a jihar Taraba bisa gano dambarwa a zaben fidda gwanin da aka gudanar
  • Wannan na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta mai zama a Yola ta yi watsi da hukuncin korar dan takarar a baya
  • A baya, babbar kotun tarayya ta soke zaben fidda gwanin gwamnan APC da aka gudanar a jihar ta Taraba

FCT, Abuja - Kotun koli ya soke zaben Emmanuel Bwacha a matsayin dan takarar gwamnan jam’iyyar APC a jihar Taraba, TheCable ta ruwaito.

Da suke yanke hukunci a ranar Laraba, alkalai biyar na kotun koli karkashin jagorancin mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun sun tabbatar da hukuncin kotun tarayya na soke zaben fidda gwanin gwamnan Taraba na APC.

A watan Satumban bara, kotun tarayya a Jalingo ya soke zaben fidda gwanin gwaman APC da ya samar Bwacha a matsayin dan takarar APC.

Kara karanta wannan

Assha: Dan takarar majalisa a jam'iyyar su Kwankwaso a Arewa ya sace N681m daga asusun banki

Kotu ta kori Bwacha daga takarar gwamnan Taraba
Kotun Koli Ta Kori Bwacha a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jihar Taraba a Jam’iyyar APC | Hoto: thecable.ng
Asali: UGC

Yadda batun shiga kotu ya faro

David Sabo Kente, daya daga cikin ‘yan takarar gwamnan APC ne ya maka Bwacha a kotu, inda ya kalubalanci sahihancin nasararsa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Simon Amobeda, alkalin kotun tarayya da ke zama a Jalingo ya amince da bukatar wanda ya shigar da kara cewa, ba a yi sahihin zaben fidda gwanin gwamna a Taraba ba.

Ya kuma yi Allah-wadai da fitar da sakamakon karya da baturen zabe ya yi a filin jirgi tare da cika wandonsa da iska zuwa kasar waje ta yi a a lokacin da aka yi zaben na fidda gwanin gwamna.

Alkalin ya umarci a sake sabon zaben fidda gwanin gwamnan APC a jihar cikin kwanaki 14, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Hukuncin baya-bayan nan

Sai dai, a ranar 24 ga watan Nuwamban bara, kotun daukaka kara a birnin Yola ya yi watsi da hukuncin babbar kotun da ta kori Bwacha.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Gwamnan CBN ya Dira Majalisar Tarayya, Ya Shiga Ganawa da Kakakin Majalisa

Amma duk da haka, Kente bai saduda ba, ta hannun lauyansa Kanu Agabi ya sake shigar da kara a gaban kotun koli.

A hukuncinta na yau, kotun koli kuwa ta kori Bwacha tare da rusa zaben, inda kotun yace an tafka kuskure a zaben na APC.

A halin da ake ciki dai, kotun koli ya yi watsi da batun kotun daukaka kara, ya tabbatar da hukuncin babbar kotun tarayya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel