Ranar 4 Ga Watan Fabrairu Za a Sake Zaben Fidda Gwanin Gwamnan PDP a Jihar Abia

Ranar 4 Ga Watan Fabrairu Za a Sake Zaben Fidda Gwanin Gwamnan PDP a Jihar Abia

  • Jam’iyyar PDP a jihar Abia ta sanar da sake fara siyar da fom din takarar gwamna a jihar da ke Kudancin Najeriya
  • Allah ya yiwa dan takarar gwamnan PDP a jihar Abia, Farfesa Uche Ikonne bayan gajeriyar rashin lafiya
  • INEC ta ba da umarnin a gaggauta sake yin zaben fidda gwani don zabo wanda zai maye gurbin dan takarar na gwamna

Jihar Abia - Jam’iyyar PDP a jihar Abia ta sanya ranar 4 ga watan Fabrairun 2023 a matsayin ranar sake yin zaben fidda gwanin dan takarar gwamnan jihar, rahoton Punch.

Wannan na zuwa ne bayan da jigon jam’iyyar kuma mai rike da tutar takarar gwamna a jihar, Farfesa Uche Ikonne ya kwanta dama a cikin makon nan.

A cikin sanarwar da jam’iyyar ta PDP ta fitar a ranar Juma’a 27 ga watan Janairu, ta ce za ta sake zaben fidda gwanin gwamnan Abia ne a filin wasa na Umuahia.

Kara karanta wannan

Dan Takarar Gwamna Ya Tsallake Rijiya da Baya a Wata Jaha, An Bayyan Jam’iyyar Da Ta Farmake Shi

PDP za ta sake zaben fidda gwanin gwamna a Abia
Ranar 4 Ga Watan Fabrairu Za a Sake Zaben Fidda Gwanin Gwamnan PDP a Jihar Abia | Hoto: vanguardngr.com
Asali: UGC

A sanarwar da PDP ta fitar ta hannun mataimakin shugabanta, Abraham Amah, jam’iyyar ta bukaci dukkan masu sha’awar tsayawa takara su siya fom din takara kafin lokacin.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

An fara siyar da fom

A cewar sanarwar, duk mai bukatar tsayawa takara zai karbi fom a hedkwatar PDP da ke Wadata Plaza a babban birnin tarayya Abuja, Channels Tv ta ruwaito.

A cewar sanarwar:

“An fara siyar da fom a ranar Juma’a, 27 ga watan Janairu kuma za a rufe a ranar Laraba 1 ga watan Fabrairun 2023.
“Za a yi taron tantance ‘yan takara a hedkwatar PDP ta kasa da ke Wadata Plaza a Abuja a ranar Alhamis, 2 ga watan Fabrairun 2023 nda misalin karfe 11 na safe.
“Ana bukatar dukkan ‘yan talarar da su gana da kwamitin manyan ayyuka na PDP a jihar Abia a ranar Juma;a 3 ga watan Fabrairun 2023 a sakateriyar jiha da ke Titin Finbars a birnin Umuahia da misalin karfe 12:00 na rana.

Kara karanta wannan

Mafita: Dan gwamnan PDP ya rasu, INEC ta fadi yadda za a maye gurbinsa

“Duk sauran bayanai da ake bukata za a fade a sakateriyar jam’iyyar ta jiha da ke titin Finbars.”

INEC ta ce a sake zaben fidda gwani cikin kwanaki 14

A tun farko kunji cewa, hukumar zabe mai zaman kanta ta ba da umarnin a sake yin zaben fidda gwanin PDP a Abia.

Za a yi hakan ne saboda Allah ya yiwa dan takarar gwamnan jihar rasuwa bayan gajeriyar rashin lafiya.

Jama’a a kasar nan sun bayyana bukatar sanin halin da ake ciki bayan mutuwar wannan dan takara na gwamna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.