Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 3 Tare da Ceto Mutane 16 da Suka Yi Garkuwa da Su a Kaduna
- Rundunar sojin Najeriya ta yi nasarar hallaka wasu ‘yan bindigan da suka addabi jama’a a jihar Kaduna
- Sojoji sun ceto wasu mutum 16 da ‘yan bindigan suka sace a wata karamar hukumar jihar ta Kaduna da ke Arewa maso Yamma
- Jihar Kaduna na daya daga cikin jihohin da ke fama da yawaitar hare-haren ‘yan bindiga, musamman a shekarunan nan
Jihar Kaduna - Dakarun sojin Najeriya karkashin rundunar Operation Forest Sanity sun ceto wasu mutane 16 da ‘yan bindiga suka sace a kananan hukumomin Birnin Gwari da Igabi a jihar Kaduna.
Hakazalika, rahoton da muke samu ya bayyana cewam sojojin sun yi nasarar hallaka ‘yan bindiga uku a ayyukan da suka yi a yankunan, Punch ta ruwaito.
Wannan na fitowa ne daga bakin kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata 24 ga watan Janairu.

Kara karanta wannan
Bayan kazamin fada da ISWAP, daruruwan 'yan Boko Haram sun mika wuya ga sojin Najeriya

Asali: UGC
A cewar sanarwar tasa, tuni aka debe wasu daga cikin wadanda aka ceto din zuwa asibiti da ke kusa a jihar.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
An kwato makamai da babura
A cewar Aruwan, kadan daga kayayyakin da aka kwato daga hannun ‘yan ta’addan sun hada da bindiga AK-47 guda daya, wata bindigar gida daya, kayan fashewa, radiyon oba-oba da babura guda 10.
A cewar sanarwar, sojoji sun amsa kiran gaggawa game da harin ‘yan bindiga a Udawa-Manini a karamar hukumar Birnin Gwari, inda suka dakile hari tare da ceto mutane 15 nan take, daya ya samu raunuka.
Haka nan, dakarun sun yi aiki irin wancan a garin Gonan Doctor da ke karamar hukumar Igabi a jihar, inda suka yi kwanton bauna a yankin Maraban Huda, Channels Tv ta ruwaito.
Gwamna ya yabawa sojoji
Kwamishinan ya ce gwamna El-Rufai ya yaba da wannan aikin, ya kuma karfafawa jami’an tsaro gwiwa bisa aikin kakkabe ‘yan ta’adda.

Kara karanta wannan
Kaico: An shiga tashin hankali, 'yan bindiga sun sace amare 2 da mutum 47 a jihar Arewa
Ya ce gwamna ya godewa irin namijin aikin da suke yi, tare da yin addu’ar Allah ya ba wadanda suka raunata lafiya cikin gaggawa.
Baya ga nasarar sojoji a Arewa maso Yamma, ana ci gaba da kai 'yan Boko Haram kasa a yankin Arewa maso Gabashin kasar nan.
Wasu da yawa ne suka mika wuya bayan samun matsala da abokan ta'addancinsu na ISWAP a jihar Borno.
Asali: Legit.ng