An Tseratar Da Wanda Akai Garkuwa Da Su A Lokacin Da Akai Garkuwa Dasu A Tashar Jirgin Kasan Edo

An Tseratar Da Wanda Akai Garkuwa Da Su A Lokacin Da Akai Garkuwa Dasu A Tashar Jirgin Kasan Edo

  • A shekarar farkon shekarar nan ne akai garkukuwa da wasu fasinjoji da suke shirin shiga jirgin kasan Edo zuwa Owerri
  • Aloakcinda akai garkuwa da su fasinjojin kusan su 42, wasu kuma suka shiga jaje a lokacin sakamakon harbe-harben da yan bindigar sukai
  • An fara ceto wasu daga cikin fasinjojin da akai garkuwa da su, inda yanzu ma aka samu kari.

Edo- Bayan shafe kusan sati daya a hannun masu garkuwa da mutane, gwamnatin jihar Edo tace an tseratar da fasinjoji goma sha biyu.

Gwamnatin tace hadin gwuiwa tsakanin jami'an tsaron kasar nan da suka hada da na DSS, Sojoji, yan sanda da kuma yan kato da gora ne suka jagoranci aikin kwato su din.

Oabaseki
An Tseratar Da Wanda Akai Garkuwa Da Su A Lokacin Da Akai Garkuwa Dasu A Tashar Jirgin Kasan Edo Hoto: Channels TV
Asali: UGC

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Jirgin Sama Cike Da Fasinjoji Ya Yi Mummunan Hatsari, Mutane Da Yawa Sun Rasu

Yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai a asibitin yan sanda na Benin, gwamnan jihar Godwin Obaseki yace akwai sakaci ga hukumomin da suke kula da jirgin kasan Nigeria kan kin yawaita jami'an tsaro a tashohin jirgin. Rahotan Vangaurad

Gwamnan yace ko sisi ba'a biya ba wajen tseratar da fasinjojin, yace aikin jami'an tsaro ne dai yasa masu garkuwa da mutanen arcewa tare da barin fasinjojin, amma yace har yanzu akwai wasu sauran da ake tunanin ma'aikatan hukumarne.

Gwmannan yace:

"Mun gode Allah, munji dadi da Allah ya bamu ikon kubutar da wadannan bayin Allah"

Ba Tsaro A Tashishin Jirgin Kasa

Gwamnan Jihar Edo yace akwai sakaci babba ga hukumomin da suke kula da jiragen kasan kasar nan.

Gwamnann yace dole ne mu nuna damuwarmu da takaicin mu kan abubuwan da suke yi na shakulatin bangaro kan tashohin da kuma su kansu jiragen.

Kara karanta wannan

Jami'an Tsaron Nigeria Sun Sanar Da Halaka Yan Ta'adda Kusan 50, Kuma Sun Kama 62

Gamwannan yace:

"In banda sakaci, ya za'ace wai mutum shida suzo su sace kusan mutum arba'in a tsahar jirgi, dole ne a bincika, sabida ba abu ne da za'a ce ya wuce shikenan ba"

Channels Tv ta rawaito cewa fasinjojin da aka kubutar an kai su asibiti, inda anan kuma aka karbi ko kuma aka samu sunayensu.

Daga cikinsu akwai Eunice Eseba, Marian Mowoe, Faith Smart, Precious Egwuje, Obehi Omaben, Amm Benson, da kuma Favour Akungo, Akhimen Ehiemamen.

Sauran sun hada da Emmanuel Esieba, Iyoha Julius and Aguelle Beatrice, sannan akwai guda biyun da kuma ba'a tseraratar da su daga hannun yan bindigar ba wanda ba'a kai da samun sunansu ba

Asali: Legit.ng

Authors:
AbdulRahman Rashida avatar

AbdulRahman Rashida