Sojoji Sun Saki Sunaye Da Hotunan Shugabannin 'Yan Ta'adda 19 Da Ake Nema Ruwa A Jallo, Tare Da Tukwicin N5m
- Hedkwatar tsaro ta Najeriya ta fitar da sunayen wasu gawurtattun shugaban yan ta'adda 19 da ta ke nema ruwa jallo saboda ayyukan ta'addanci
- Rundunar sojojin ta Najeriya ta bayyana cewa yan ta'addan sun dade suna adabar jihohin arewa maso gabas, arewa maso yamma, da arewa ta tsakiya
- Rundunar ta yi alkawarin bada tukwicin zunzurutun kudi Naira miliyan 5 ga duk dan Najeriya da ya bada bayanai da suka yi sanadin kama kowanne cikinsu
FCT, Abuja - Hedkwatar tsaro ta Najeriya, a ranar Litinin ta fitar da sunayen kwamandojin yan ta'adda 19 da ke adabar yankunan Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya a kasar, rahoton Daily Trust.
Hedkwatar tsaron ta ce za ta ba'ada tukwicin Naira miliyan 5 ga duk wani dan Najeriya da ya bada bayanan yadda za a kama yan ta'addan, ta bukaci al'umma su tuntube ta a wannan lambar 09135904467.

Kara karanta wannan
Karin Bayani: Babbar Mota Ta Murkushe Motocin Ayarin Gwamnan Arewa, Ya Sha Da Kyar

Asali: Twitter
Ta ce hakan ya zama wajibi ne domin cigaba da kawar da abokan gaban, inda ta kara da cewa hakan yunkuri ne na dawo da zaman lafiya gaba daya a kasar, rahoton LIB.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Sunayen yan ta'addan da ake nema ruwa a jallo da Direkta na sashen watsa labarai na hedkwatar tsaro, Manjo Janar Jimmy Akpor ya fitar sune:
Sunayen kwamandojin 'yan ta'adda 19 da sojojin Najeriya ke nema ruwa a jallo
- Sani Dangote – Asalinsa: Kauyen Dumbarum . Karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.
- Bello Turji Gudda – Asalinsa: Kauyen Fakai na Jihar Zamfara.
- Leko – Asalinsa: Kauyen Mozoj, Karamar Hukumar Mutazu ta jihar Katsina.
- Dogo Nahali – Asalinsa: Kauyen Yar Tsamiyar Jno. Karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina.
- Halilu Sububu – Asalinsa: Kauyen Sububu a karamar hukumar Maradun na jihar Zamfara.
- Nagona – : Asalinsa: Kauyen Galadima a Isa Loa na jihar Sokoto.
- Nasanda – : Asalinsa, Kauyen Village a karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.
- Isiya Kwashen Garwa – Asalinsa: Kauyen Kamfanin Daudawa na karamar hukumar Faskari, Jihar Katsina.
- Ali Kachallaa da aka fi sani da Ali Kawaje – Asalinsa: Kauyen Kuyambara da ke karamar hukumar Danaadau Maru na jihar Zamfara.
- Abu Radde – Asalinsa: Kauyen Varanda da ke karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina.
- Dan-Da – Asalinsa: Kauyen Varanda da ke karamar hukumar Batsari na jihar Katsina.
- Sani Gurgu – Asalinsa: Kauyen Varanda da ke karamar hukumar Batsari ta Jihar Katsina.
- Umaru Dan Najeriya – Asalinsa: Kauyen Rafi. Garin Mada a Gusaulaga.
- Nagala – Asalinsa: Karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara.
- Alhaji Ado Aliero – Asalinsa: Kauyen Yankuzo da ke karamar hukumar Tsafe na jihar Zamfara.
- Monere – Asalinsa: Kauyen Yantumaki , karamar hukumar Dan na jihar Katsina.
- Gwaska Dankarami – Asalinsa: Kauyen Shamushele da ke karamar hukumar Zuri na jihar Zamfara.
- Baleri – Asalinsa: Karamar hukumar Shinkafi na jihar Zamfara.
- Mamudu Tainange – Asalinsa: Kauyen Varanda a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina.

Kara karanta wannan
Najeriya Ta Zo Lamba 1 A Jerin Kasashen Duniya Da Aka fi Shan Wiwi: Buba Marwa Ya Tabbatar da Rahoton UN
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’addan Boko Haram/ISWAP 60, Sun Kama Wasu Fiye da 90, DHQ
A wani rahoton, hedkwatar tsaro ta Najeriya ta bayyana a ranar Alhamis 2 ga watan Nuwamba cewa, jami'an sojojin kasar sun yi ayyukan kakkabe 'yan ta'addan Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas.
Sanarwar da hedkwatar ta fitar ta bayyana cewa, akalla 'yan ta'adda 60 na Boko Haram/ISWAP jami'an sojoji suka hallaka, yayin da aka kama wasu 90 daga 'yan ta'addan.
Asali: Legit.ng