Yadda Gwamnan PDP Ya Rabawa Jihohi 5 Gudumuwar Naira Biliyan 2 a Shekara 1

Yadda Gwamnan PDP Ya Rabawa Jihohi 5 Gudumuwar Naira Biliyan 2 a Shekara 1

  • Abin da Nyesom Wike ya bada a matsayin kyauta ko kuma tallafi daga bara zuwa yanzu ya zarce N2bn
  • Gwamnan ya kashewa jihohin Sokoto, Kaduna da Legas Naira biliyan 2.1 a shekara da ‘yan watanni
  • Nyesom Wike ya yi rabon kudi har a Arewacin Najeriya a lokacin da musiba ta aukawa mazauna yankin

Port Harcourt, Rivers – Mai girma Gwamna Nyesom Wike mai mulkin jihar Ribas ya saba taimakawa jihohi da daidaikun mutane da-dama da tallafin kudi.

Mun fahimci a watanni 15 da suka wuce, gwamnan na Ribas ya bada gudumuwar Naira biliyan 2.1 ga jihohin da bukata ta taso masu a fadin kasar nan.

Punch ta bi yadda gwamnan ya raba gudumuwa daga watan Junairun 2021 zuwa Oktoban nan.

1. Jihar Sokoto

A lokacin da gobara ta ci babbar kasuwar Sokoto, Gwamnan Ribas ya tallafawa Gwamna Aminu Tambuwal da kyautar N500m a ranar 10 ga Junairun 2021.

Kara karanta wannan

Anambra da Jihohi 7 da Peter Obi Zai Iya Yi wa Atiku Lahani a Zaben Shugaban kasa

Gwamna Atiku Bagudu mai makwabtaka da Sokoto, ya ba ‘yan kasuwar gudumuwar N30m a lokacin.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

2. Jihar Akwa Ibom

Nyesom Wike ya bada kyautar N600m ga jihar Akwa Ibom a Mayun 2021. Gwamnan ya bada kudi wajen gina asibitin koyar da likitoci da ke Awa a garin Onna.

Nyesom Wike
Gwamna Nyesom Wike da Sarkin Musulmi Hoto: pmnewsnigeria.com
Source: UGC

3. Jihar Bayelsa

Kokarin gwamnan bai tsaya nan ba, ya bada N500m domin a gina jami’ar aikin likitanci a garin Yenagoa. An yi wannan a watan Fubrairun shekarar nan.

4. Jihar Kaduna

Da Gwamnan ya zo Kaduna domin yakin neman zama ‘dan takaran PDP a 2023, ya bada gudumuwar N200m domin kula da wadanda rikicin ‘yan bindiga ya ci.

5. Jihar Legas

A makon jiya Nyesom Wike ya ziyarci Legas, nan ma ya raba N300m ga matan jami’an gwamnatin Legas, yace ya yi hakan domin yabawa ayyukan da ake yi.

Lissafin LP a zaben 2023

Kun ji labari takarar Peter Obi a zaben sabon shugaban kasa tana cigaba da motsa siyasa, musamman ganin yadda Obi ya samu karbuwa a Kudancin Najeriya.

Kara karanta wannan

Rudani: Gwamnan PDP mai ba Atiku ciwon kai ya zabo tsohon jigon APC ya zama kwamishinansa

Ana hasashen Jam’iyyar Labour Party za ta gwagwiyi kuri’un da Atiku Abubakar ya samu a 2019. Wannan tasiri zai iya aiki har a wasu jihohin da ke Arewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng