Gwamna Zulum Na Borno Ya Yi Muhimmin Nadi A Gwamnatinsa

Gwamna Zulum Na Borno Ya Yi Muhimmin Nadi A Gwamnatinsa

  • Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya amince da nadin Baba Bura Usman a matsayin sabon akanta janar na Jihar Borno
  • Malam Isa Gusau, mai magana da yawun gwamnan na Jihar Borno ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba
  • Baba Bura Usman, wanda kwararre ne a bangaren kudi zai maye gurbin Mai Adamu Ya'u wanda ya yi murabus a baya-bayan nan

Borno - Gwamna Babagana Zulum na Jihar Borno ya amince da nadin Baba Bura Usman a matsayin sabon akanta janar na Jihar Borno.

Mai magana da yawun gwamnan, Malam Isa Gusau ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Laraba.

Taswirra Jihar Borno
Gwamna Zulum Na Borno Ya Yi Muhimmin Nadi A Gwamnatinsa. Hoto: @MobilePunch.
Asali: Facebook

Kara karanta wannan

Kano: Jami'an NSCDC an Kama Matashi Ya Kuntuka Sata a Masallaci

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kafin nadinsa, Bura shine direktan fanin ajiyar kudi a Ma'aikatar Kudi da Tsare-Tsare na Jihar Borno tun shekarar 2020 in ji Gusau.

Usman, dan shekara 57, dan asalin karamar hukumar Kaga ne a arewacin Borno, ya shafe kimanin shekara 20 yana aiki a bangaren kudi a cewar sanarwar.

Wasu daga cikin wuraren da Usman ya yi aiki a baya

Ta kara da cewa akanta janar din, tun 1990, ya yi aiki a matsayin mataimakin akanta a wani kamfani mai zaman kansa, Premier Property Dev. Co. Ltd, kafin ya fara aiki da gwamnatin jihar Borno a matsayin babban akanta a Cibiyar Al'adu da ke Maiduguri a 1998.

Usman ne babban akanta a gidan gwamnati a Maiduguri a 2021 kuma shine babban akanta a sashin kasafi da tsare-tsare a 2003, a Hukumar Ilimi Bai Daya Na Borno a 2010 da kuma Hukumar Fansho ta Borno a 2017 kafin ya zama direkta a hukumar fansho a 2017, a cewar sanarwar.

Kara karanta wannan

Wani Matashi Dan Shekara 17 Ya Nutse A Kududufi A Jihar Kano

Usman ya kuma yi wasu ayyukan da dama a ma'aikatu da hukumomin gwamnatin a Borno.

Takaitaccen tarihin karatun Usman

Usman yana da babban diploma ta kasa (Hnd) a bangaren kula da kasuwanci daga Kwalejin Ilimi Ta Ramat, Maiduguri.

Usman ya yi kwasa-kwasai a bangaren kula da kudade a Najeriya da Hadadiyar Daular Larabawa, UAE, kuma yana da satifiket a bangaren kula da kudade, fasahar sadarwa da akanta ,IPSAS, da ilimin kwamfuta.

Sabon akanta janar din kuma mamba ne a kungiyar akantoci ta Najeriya (ANAN) da wasu kungiyoyin.

Usman zai karbi aiki ne daga hanun Mai Adamu Ya'u wanda ya yi murabus a baya-bayan nan.

Borno: Zulum Ya Biya Naira Miliyan 5 Don Daukan Nauyin Karatun Wani Hazikin Yaro Mai Shekara 13 a Maiduguri

A wani rahoton, Gwamna Zulum na Jihar Borno ya bada N5m ga wata makaranta mai zaman kanta domin daukan nauyin karatun Musa Sani, yaro dan shekara 13 mai hazaka a Borno wanda ya yi amfani da laka ya kwaikwayi ginin gadan sama ta farko a jihar da ke custom round about a Maiduguri.

Kara karanta wannan

Gyaran birni: Buhari ya amince a kashe N28bn don yin wasu manyan ayyuka a Abuja

An biya kudin ne ga hukumar makarantar Golden Olive Academy, Maiduguri, domin daukan nauyin karatun Musa daga ajin frimare na hudu har kammala babban sakandare, Nigerian Tribune ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel