Da dumi-dumi: ‘Yan ta’adda sun kai farmaki a jihar Neja, sun sace mutane da dama

Da dumi-dumi: ‘Yan ta’adda sun kai farmaki a jihar Neja, sun sace mutane da dama

Wani rahoton da jaridar Punch ya fitar ya ce, wasu 'yan ta'adda sun yi garkuwa da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba a jihar Neja.

Rahoton ya tattaro cewa, an ce ‘yan ta’addan sun kai farmaki a unguwar Daza da ke karamar hukumar Munya ta jihar, inda suka yi ta harbe-harbe ba kakkautawa.

Yadda 'yan ta'adda suka farmaki jihar Neja
Da dumi-dumi: ‘Yan ta’adda sun kai farmaki a jihar Neja, sun sace mutane da dama | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Mazauna garin da dama sun tsere daga yankin sakamakon harin da aka kai a daren jiya Alhamis.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Online view pixel