Jerin Sunaye: Shugabannin Ƴan Ta’adda da Ƴan Bindiga Da Aka Kashe Daga Farkon Shekarar 2021 Zuwa Yanzu

Jerin Sunaye: Shugabannin Ƴan Ta’adda da Ƴan Bindiga Da Aka Kashe Daga Farkon Shekarar 2021 Zuwa Yanzu

Duk da cewa har yanzu ba a kawo karshen yaki da ta'addanci ba a Nigeria, an samu wasu cigaba a shekarar 2021.

Kawo yanzu, an kashe a kalla shugabannin yan bindiga da yan ta'adda 12 a yayin da hukumomin tsaro ke cigaba da yaki da bata garin da ke adabar kasar.

Jerin Sunaye: Shugabannin 'Yan Ta'adda da 'Yan Bindiga da aka kashe daga farkon shekarar 2021 zuwa yanzu
Sojojin Nigeria da aka gani suna tafiya cikon motarsu a Ngamdu, Nigeria, a ranar 3 ga watan Nuwamban 2020. Hoto: Audu Marte/AFP
Asali: Getty Images

Ga dai jerin sunayen shugabannin yan ta'addan da aka kashe a shekarar 2021 bisa sanarwar da rundunar sojojin Nigeria da rahotonni da sauran kafafen watsa labarai ke fitarwa.

1. Abubakar Shekau

Bayan shekaru da dama ana ayyana cewa ya mutu amma ya sake bulowa, daga karshe an ruwaito cewa an kashe Abubakar Shekau, shugban kungiyar Boko Haram a watan Mayu.

Kara karanta wannan

Da duminsa: Bayan harin yan ta'adda, jirgin kasan Abuja/Kaduna zai koma aiki ranar Asabar

A cewar The Cable, dan sanda mai binciken sirri ya ambato cewa kwamandojin kungiyar ISWAP, kungiyar ta da balle daga Boko Haram, na cewa Shekau ya kashe kansa da bam "lokacin da ya lura mayakan ISWAP ne son kama shi da ransa."

2. Abu Mus'ab Albarnawi

A ranar A;hamis, 14 ga watan Oktoba, babban hafsan tsaro na kasa, CDS, Janar Lucky Irabor ya tabbatar da kashe shugaban ISWAP, Abu Mus'ab Albarnawi.

Al-Barnawi dan wanda ya kafa Boko Haram ne, Muhammad Yusuf wanda shima yan sanda sun kashe shi a 2009 a farkon lokacin da kungiyar ke kafuwa.

3. Yaya Ebraheem

PR Nigeria ta ruwaito cewa Yaya Ebraheem na daya daga cikin kwamandojin ISWAP da ya yi yunkurin kai wa tawagar sojoji hari na ranar Laraba 13 ga watan Oktoba a Ngamdu a Borno. Amma, shima an ruwaito cewa sojoji sun kashe shi.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: ‘Yan bindiga sun cinna wuta a fadar sarkin Imo

4. Baba Chattimari

Baba Chattimari, kwamandan ISWAP, shima an ruwaito cewa an kashe shi tare da Ebraheem.

5. Abu Adam Oubaida

Abu Adam Oubaida shine kwamandan ISWAP na uku da aka ruwaito cewa sojoji sun kashe a yankin Ngamdu.

6. Auwalun Daudawa

Auwalun Daudawa hatsabibin dan bindiga ne wanda ya jagoranci sace dalibai 300 na makarantar sakandare ta Kankara a jihar Katsina a Disamban 2020.

A watan Fabrairun 2021, Daudawa ya ajiye makamansa ya rungumi shirin sulhu na Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle.

Amma, kwanaki kadan bayan mika wuyarsa ya koma daji ya cigaba da laifukansa da ya saba.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Zamfara, Abubakar Dauran ya ce Daurawa ya shaidawa wasu mutane cewa zai tafi daurin auren wasu yan uwansa ne.

Sai dai, ya sashe shanu fiye da 100 ya kashe mai kiwonsu, a cewar kwamishinan. Wasu mutane a yankin sun mayar da martani sun halaka shi kamar yadda Channels TV ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Yan IPOB sun kai hari ofishohin yan sanda 164, sun kashe jami'ai 175, duka laifin Nnamdi Kanu ne: FG

Amma a rahoton da Daily Trust ta wallafa, an kashe Daudawa ne yayin musayar wuta da wata kungiyar yan bindigan masu gaba da shi a tsakanin karamar hukumar Zurmi a Katsina da Batsari a Katsina.

7. Jauro Daji

Jauro Daji shima wani hatsabibin dan bindiga ne da ya dade yana adabar mutanen jihar Niger.

Yan sanda, tare da taimakon yan banga sun kashe Daji da wasu yan bindigan da dama masu masa biyaya a yankin Kontagora na jihar a ranar Litinin 30 ga watan Agusta.

8. Habu Nabayye

9. Isuhu Sadi

10. Murtala Danmaje

Nabayye, Sadi da Danmaje shugabannin yan bindiga ne a jihar Zamfara. A cewar PR Nigeria, sojojin saman Nigeria ne suka kashe su yayin ruwan wuta da suka yi a dajin Kuyanbana.

11. Alhaji Karki Buzu

12. Yalo Nagoshi

PR Nigeria ta rahoto cewa an kashe Buzu da Nagoshi a watan Oktoba a jihar Niger. An ce suna cikin yan bindiga 32 da suka tsere daga Zamfara kafin dakarun sojojin Nigeria suka katse musu hanzari.

Kara karanta wannan

Jami’an DSS, ‘yan sanda, sojoji sun kewaye kotun Abuja a shari’ar Nnamdi Kanu

Yunwa ya saka 'yan bindiga a gaba, sun nemi a basu dafaffen abinci a matsayin kudin fansa

A wani labarin, kun ji cewa Ƴan bindiga a ƙaramar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna sun fara tambayar dafaffen abinci a matsayin kuɗin fansa, rahoton Daily Trust.

Ƴan bindigan sun janye kai hare-hare a garuruwa tun bayan da gwamnatin jihar ta soke cin kasuwannin mako-mako don daƙile rashin tsaro.

Wani shugaban matasa a ɗaya daga cikin ƙauyukan Birnin Gwari, Babangida Yaro ya shaidawa Daily Trust cewa tun bayan hana cin kasuwanni ƴan bindiga da ke sace mutane a ƙauyukan Kutemashi da Kuyello dafaffen abinci suke tambaya duk lokacin da suka sace mutane.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel