Labari da ɗuminsa: Gwamnatin Kogi ta naɗa sabon Attah na Igala

Labari da ɗuminsa: Gwamnatin Kogi ta naɗa sabon Attah na Igala

  • Majalisar kolin jihar Kogi ta amince da nada Prince Mathew Alhaji Opaluwa a matsayin Attah na Igala
  • Majalisar ta amince da nadin sabon basaraken ne yayin taronta karo na 6 da ta gudanar a ranar Litinin a Lokoja
  • Kafin nadinsa, Prince Mathew Alhaji Opaluwa mataimakin direkta ne na hukumar zabe mai zaman kanta INEC

Jihar Kogi - Majalisar koli na jihar Kogi ta amince da nadin Prince Mathew Alhaji Opaluwa a matsayin Attah na masarautar Igala kamar yadda The Sun ta ruwaito.

Majalisar ta bada amincewarta ne yayin taronta na 6 da aka yi a dakin taronta a gidan gwamnatin jihar da ke Lokoja a ranar Litinin.

Labari da ɗuminsa: Gwamnatin Kogi ta naɗa sabon Attah na Igala
Prince Mathew Alhaji Opaluwa. Hoto: Daily Trust
Source: Facebook

Daily Trust ta ruwaito cewa Opaluwa shine na tara cikin 16 kuma na hudu cikin 'ya'ya maza na marigayi Cif Opaluwa na gidan saurauta na Aju Ameacho a masarautar Igala.

Kara karanta wannan

Da duminsa: 'Yan bindiga sun kai farmaki, sun sace limamin cocin katolika

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Takaitaccen tarihin sabon basaraken

Sabon Attah da aka nada ya fara karatunsa ne a St Boniface Primary School, Idah a 1975 sannan ya yi gaba zuwa St Peter’s College, Idah inda ya samu shaidar kammala sakandare ta West African School Certificate (WASC), a 1980.

Ya hallarci makarantar sharen fage da ke Ugbokolo a jihar Benue a 1981 sannan ya tafi Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a wannan shekarar ya samu digiri a bangaren nazarin kasuwanci a 1986.

Kazalika, ya yi digiri na uku (MBA) a bangaren koyan dabarun kasuwanci a 1997.

Kafin nadinsa, ya yi aiki a hukumar zabe mai zaman kanta INEC a 1988 har ya samu karin girma ya zama mataimakin direkta.

Ya yi aiki a wurare da dama a kananan hukumomin jihar Kogi, Kaduna da babban birnin tarayya Abuja a matsayin jami'in zabe yayin da a Katsina shine ke kula da sashin bincike da adana bayanai na hukumar zaben.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164