Yayin da Ta Ke Tsaka da Yaki da Iran, Isra’ila Ta Fadi Kasar da Za Ta Mamaye
- Ministan tsaron Israa, Israel Katz ya yi magana kan shirin da Isra’ila ke yi na mamaye wasu yankunan kudancin Lebanon
- Katz ya bayyana kudirin kafa yankin tsaro har zuwa kogin Litani tare da ci gaba da ikon tsaro domin fadada ikonta
- Ya ce za a hana mazauna yankin dawowa, tare da rusa gidaje kamar yadda aka yi a Gaza wanda ya jawo magana
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Tel Aviv, Israel - Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya yi magana game da ci gaba da yaki a Gabas ta Tsakiya.
Katz ya bayyana cewa sojojin kasar na shirin mamaye wasu yankunan kudancin Lebanon ko bayan kammala yakin da suke yi da kungiyar Hezbollah.

Source: Facebook
A cikin wani bidiyo da ya fitar wanda Al Jazeera ta samu, Katz ya bayyana cewa ana shirin kafa wani yankin tsaro na dindindin a cikin kasar Lebanon, wanda zai kai har zuwa kogin Litani.
Asarar da aka yi a yakin Iran/Isra'ila
Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da yakin kasar Iran da Isra'ila tare da goyon bayan Amurka karkashin Donald Trump.
A ranar 28 ga watan Fabrairun shekarar 2026 Isra'ila da Amurka suka kai hari a birnin Tehran wanda ya yi barna da jawo asarar rayuka.
Harin ya yi sanadiyyar mutuwar jagoran addini a Iran, Ayatollah Ali Khamenei da wasu manyan jami'an tsaron kasar.
Daga bisani, Iran ta mayar da martani mai zafi inda ta lahanta Isra'ila da Amurka wanda har yanzu ake ci gaba da yaki.

Source: Getty Images
Abin da sojojin Isra'ila ke shirin yi
Katz ya ce sojojin kasar Isra'ila za su kafa sansanin tsaro a cikin wasu yankunan Lebanon domin karfafa ikon tsaro a wurin.
Ya ce:
“A karshen wannan aiki, rundunar sojin Isra’ila za ta kafa kanta a yankin tsaro a cikin Lebanon, kuma za ta ci gaba da rike ikon tsaro a duk yankin har zuwa kogin Litani.”
Ministan ya kuma ce za a hana mazauna Lebanon da aka raba da muhallansu komawa yankunansu bayan yaki, cewar Times of Israel.
Ya kara da cewa za a aiwatar da irin tsarin da aka yi a Gaza, inda aka rusa gidaje a yankunan kan iyaka.
“A dukkan gidajen da ke kauyukan da ke kusa da iyaka a Lebanon za a rushe su bisa tsarin da aka yi a Rafah da Beit Hanoon a Gaza."
- Israel Katz
Yakin Iran: Fafaroma ya shawarci Isra'ila da Amurka
Tun farko, kun ji cewa Shugaban darikar Katolika na duniya, Fafaroma Leo XIV ya yi sake yin magana game da yakin Iran da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya.
Fafaroma ya ce Allah ba ya karɓar addu’o’in shugabannin da ke tayar da yaƙe-yaƙe, yana mai cewa hannayensu sun cika da jini.
Yayin bikin Palm Sunday, ya ce Yesu mai son zaman lafiya ne, kuma ba za a yi amfani da shi wajen halatta yaƙi ba inda ya tabbatar da matsalar da ke tattare da haka.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

