An ‘Gano’ Musabbabin Hari kan Musulmi bayan Farmaki ana Sallar Asham a Ramadan

An ‘Gano’ Musabbabin Hari kan Musulmi bayan Farmaki ana Sallar Asham a Ramadan

  • An kai hari domin kona ginin cibiyar al’ummar Musulmi da gangan kusa da sabon masallaci a Worcester, Birtaniya
  • Ƙungiyar 'Worcester Muslim Welfare Association' ta ce harin ya jefa al’umma cikin matsanancin damuwa a watan Ramadan
  • Lamarin ya biyo bayan wani hari a masallacin Manchester, inda aka kama mutum ɗaya yayin da ake farautar wani da ake zargi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Worchester, England - Wata cibiyar al’ummar Musulmi da ke kusa da sabon masallaci a garin Worcester ta magantu kan harin da aka kai.

An kai harin ne a yankin Yammacin Midlands na ƙasar England wanda ya fuskanci abin da aka bayyana a matsayin “tayar da gobara da gangan.”

An kai hari a masallacin Manchester
Babban masallacin birnin Manchester da ke kasar Burtaniya Hoto: Getty Images.
Source: Getty Images

Musulmai sun magantu kan hari a cibiyarsu

Ƙungiyar Worcester Muslim Welfare Association (WMWA) ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis 26 ga watan Fabrairun 2026 wanda shafin @5Pillarsuk ya wallafa a X.

Kara karanta wannan

Kisan masu sallar tarawihi a masallaci ya tayar da hankali, ana ta magana

A cikin sanarwar, kungiyar ta ce wani namiji ne ya kai harin da safe, inda ya nufi ginin al’umma da ke kusa da masallacin.

A cewar ƙungiyar, ginin da aka kai wa harin shi ne 'Unity House Community Hub' da ke kan titin Stanley a Worcester, wanda aka ƙona da gangan.

Bidiyoyi da ke yawo a kafafen sada zumunta sun nuna wani mutum yana kunna wuta kusa da ginin kafin ya tsere daga wurin.

An kai hari kan Musulmi kusa da masallaci a Birtaniya
Cibiyar Musulunci da aka yi yunkurin konawa a Worcester da ke Birtaniya. Hoto: BBC.
Source: Facebook

Matakin farko da Musulmi suka dauka

Ƙungiyar ta ce ta kai rahoton lamarin ga rundunar yan sanda na Yammacin Mercia, tana mai cewa harin ya haddasa “mummunar damuwa a tsakanin al’ummarmu.”

Sanarwar ta ƙara da cewa:

“Ba za mu iya kallon wannan lamari a matsayin abu daban ba."
“Mun yi imanin cewa wannan hari ne na ƙiyayya mai tushe a kan wariyar launin fata da addini da ake yawan kai wa Musulmi.”

Kungiyar ta ce tana mai tunatar da cewa lamarin ya faru ne a cikin watan Ramadan mai alfarma bayan wani mummunan hari da aka kai a wani hari a masallaci a Manchester.

Kara karanta wannan

Kisan matafiya a Plateau: Gwamna ya ba da umarni bayan tsoron barkewar rikici

Ƙungiyar ta ce tana da yakinin cewa harin na ɗauke da ƙiyayya ta ɓangaren launin fata da addini, watau 'Islamophobia'.

A Manchester kuwa, ‘yan sanda sun kama mutum ɗaya tare da fara farautar wani a ranar Laraba 26 ga watan Fabrairun shekarar 2026 bayan kai harin.

Hakan ya biyo bayan zarginsa da shigar da makamai ciki har da gatari da wuka a cikin babban masallacin Manchester yayin sallar Tarawihi.

Firayim minista ya magantu kan hari a masallaci

A wani labarin, Firayim ministan Birtaniya, Keir Starmer ya yi magana game da wani mutum da aka kama da makami yana shirin shiga masallaci a birnin Manchester.

Keir Starmer ya bayyana matakan tsaro da za a cigaba da dauka a masallatai domin kare Musulmai masu ibada, musamman a watan azumin Ramadan.

Jami'an tsaron Birtaniya sun bayyana cewa ana yi wa wanda aka kama tambayoy domin sanin dalilin yunkurin shiga masallaci da makamai a Birtaniya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.