UAE: Daular Larabawa Ta Gamu da Mummunan Iftila'i, Al'amura Sun Tsaya Cak a Birane

UAE: Daular Larabawa Ta Gamu da Mummunan Iftila'i, Al'amura Sun Tsaya Cak a Birane

  • Mamakon ruwan sama da ya sauka ya jawo ambaliya a Dubai da Sharjah, lamarin da ya haddasa sokewa da jinkirta tashin jiragen sama
  • Kamfanoni da filayen jiragen sama sun fuskanci matsala yayin da hanyoyi suka cika da ruwa, wanda ya tilasta hakura da zirga zirga
  • Wannan lamari ya tuno da mummunar ambaliyar da ta afku a Daular Larabawa a 2024 bayan saukar ruwa mafi yawa a tarihin kasar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Dubai - Hukumomin filayen jiragen sama a Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) sun soke ko jinkirta tashin jirage da dama bayan afkuwar mummunar ambaliyar ruwa.

An ce wani mamakon ruwan sama mafi karfi da ya sauka a kasar a ranar Juma’a ne ya hadda ambaliyar da ta nutsar da hanyoyi a manyan birane.

Ruwa da ambaliyar ruwa sun jawo tsaikon zirga-zirgar jiragen sama a Hadaddiyar Daular Larabawa.
Yadda ruwan sama ya mamaye tituna a wani yanki na Hadaddiyar Daular Larabawa. Hoto:Anadolu / Contributor
Source: Getty Images

An samu ambaliyar ruwa a Daular Larabawa

Kara karanta wannan

Wuta ta tashi bayan fetur ya kwarara gidaje a hadarin tankar mai

Kamfanin jiragen sama na Emirates da ke Dubai ya soke tashin jiragensa 13 a ranar Juma’a, 19 ga Disamba, 2025, in ji rahoton Channels TV.

An kuma samu jinkiri da karin soke tashin jirage a filin jirgin saman Sharjah sakamakon ruwan sama da aka yi tun da daddare, wanda ya zo hade da walƙiya da tsawa mai karfi.

A Sharjah, babbar hanya ta birnin ta cika da ruwa da sassafe, inda aka ga mutane sun cire takalmansu, suna tafiya cikin ruwan a hankali.

An kuma hango wani mutum a saman kekensa yana kokarin tsallaka titi, wanda ruwan ya shanye tayoyin kekensa, alamar da ke nuna zurfin ruwan.

Ambaliya ta tilasta mutane zaman gida

Abubuwan da suka faru sun tuna wa mutane irin ambaliyar da ta afku a daular a watan Afrilun 2024, lokacin da ruwan sama mafi yawa a tarihi ya haddasa cunkoso da soke fiye da jirage 2,000 a babban filin jirgin saman Dubai.

Tun a ranar Alhamis, ‘yan sandan Dubai suka gargadi mazauna biranen daular da su zauna a gida sai idan akwai bukatar fita ta gaggawa, yayin da ake sa ran zuwan mamakon ruwan sama.

Kara karanta wannan

Bayan suka ta ko ina, an dakatar da yi wa dogarin Shugaba Tinubu karin girma

Da Asubar ranar Juma’a, an ga motocin tsaftace muhalli suna aiki a sassan Dubai domin share hanyoyin da suka toshe manyan magudanun ruwa, in ji rahoton Punch.

Ambaliyar ruwa ta mamaye wasu birane na Daular Larabawa.
Mutane na kokarin tsallake titi yayin da ambaliya ta shafe tituna a Daular Larabawa. Hoto: FADEL SENNA / Contributor
Source: Getty Images

An hango mamakon ruwa a kasar UAE

Shafin yanar gizon Filayen Jiragen Sama na Dubai ya nuna cewa an samu jinkirin tashin jirage da dama, yayin da aka soke tashin wasu.

Ofishin mai magana da yawun filayen jiragen saman Dubai ya ce an soke ko kuma an jinkirta tashin wasu jirage ne sakamakon yanayi mara kyau.

Cibiyar kula da yanayi ta UAE ta riga ta yi gargadin cewa za a samu ruwan sama daga Alhamis zuwa Juma’a a sassan kasar, ciki har da Dubai da babban birnin kasar, Abu Dhabi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com