Ta Faru Ta Ƙare, Donald Trump Ya Hana Ƴan Ƙasashe 19 Shiga Amurka, An Saki Sunaye

Ta Faru Ta Ƙare, Donald Trump Ya Hana Ƴan Ƙasashe 19 Shiga Amurka, An Saki Sunaye

  • Gwamnatin Donald Trump ta dakatar da karɓar dukkan 'yan hijira daga ‘yan ƙasashe 19, tana mai cewa tsaron Amurka ya fi komai muhimmanci
  • Sabon takunkumin ya shafi masu neman Green Card da shaida zama 'yan Amurka, musamman daga ƙasashen da aka sanya wa takunkumi
  • Matakin ya biyo bayan harin da wani ɗan Afghanistan ya kai wa sojojin Amurka a Washington, abin da ya harzuka Trump kan bakin kasar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Amurka - Gwamnatin Donald Trump, ta ba da umarnin gaggawa na dakatar da karbar dukkanin sababbin takardun neman izinin shiga Amurka daga ƙasashe 19.

Wannan matakin ya fito ne daga wata takarda mai shafuka huɗu da hukumar shige da fice da ba da izinin zama a Amurka USCIS ta fitar a ranar Talata.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi awon gaba da amarya da sauran 'yan biki a Sokoto

Gwamnatin Trump ta hana shigowar mutane daga kasashe 19
Shugaba Donald Trump ya sha alwashin gyara Amurka a lokacin yakin neman zabensa. Hoto: @realDonaldTrump
Source: Twitter

An hana 'yan kasashe 19 shiga Amurka

A cewar USCIS, dakatarwar ta shafi masu neman katin kasar, da masu neman izinin zama 'yan Amurka, tare da jaddada cewa an ɗauki wannan mataki ne don ƙara tsaurara binciken tsaro, in ji rahoton Reuters.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Takardar ta ce:

“Mun fahimci cewa wannan mataki zai iya janyo tsaiko ga wasu aikace-aikace na masu son shiga Amurka. Amma wannan jinkiri ya dace idan aka kwatanta da wajibcin kare tsaron ƙasa.”

Matakin ya shafi ‘yan ƙasashe 19 da Trump ya saka wa takunkumin shiga Amurka tun watan Yuni, ciki har da:

  • Afghanistan
  • Iran
  • Libya
  • Somalia
  • Sudan
  • Yemen

Sai kuma wasu ƙarin ƙasashe bakwai da ke ƙarƙashin takumkumi na musamman, ciki har da:

  • Cuba
  • Laos
  • Sierra Leone
  • Venezuela

Matakin Trump bayan harin Washington DC

Trump ya dauki wannan mataki ne kwanaki kaɗan bayan da wani mutumi ya bude wa sojojin kasar biyu wuta, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar ɗaya, ɗaya kuma ya jikkata sosai.

Kara karanta wannan

Tashin hankali a Kano: Mummunar gobara ta cinye shaguna 500 a wata babbar kasuwa

An gurfanar da wanda ake zargi — dan asalin Afghanistan wanda ya shiga Amurka a zamanin gwamnatin Biden — a kotu ranar Talata, inda ya ce bai aikata laifin komai ba.

Rahotannin NBC sun nuna cewa hukumar ta yi gargadin cewa tun da akwai shari’o’in neman mafaka sama da miliyan 1.4, akwai yiwuwar wannan dakatarwa ta janyo dogon tsaiko ga dubban mutane.

Kakakin USCIS ba ta mayar da martani kan tambayoyin manema labarai ba zuwa daren Talata, 2 ga watan Disamba, 2025.

Shugaba Donald Trump ya hana kasashe 19 shiga Amurka bayan harin Washington DC.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya na aiki a ofishinsa da ke White House. Hoto: @realDonaldTrump
Source: Facebook

Hukumomi sun goyi bayan karin takunkumi

Daraktan USCIS, Joseph Edlow, ya soki tsarin tantance ‘yan Afghanistan da suka shigo bayan janyewar Amurka daga ƙasar a 2021, yana mai cewa:

“Ba a tantance su yadda ya kamata ba.”

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida (DHS), ƙarƙashin Kristi Noem, ta yi kira da a ƙara tsaurara matakan shigar bakin haure kasar.

A wani sako da ta wallafa a shafinta na X, Kristi Noem ta ce:

“Na gana da shugaban kasa.
"Na ba da shawarar a dauki cikakken takunkumi ga duk wata ƙasa da ke turo mana da masu aikata laifi, masu dogaro da taimakonmu, da masu zamar mana kaska a kasa.”

Kara karanta wannan

'Third World': Najeriya da kasashe 62 da Trump zai hana mutanensu zama a Amurka

Trump zai dauki mataki kan 'Third World'

A wani labari, mun ruwaito cewa, Donald Trump ya ce tsarin hijira zuwa Amurka ya haddasa matsaloli ga tsaro, da cunkuso a makarantu, asibitoci da gidaje.

Trump ya yi misali da jihar Minnesota, inda ya ce ce ’yan hijira daga Somalia sun canja tsarin rayuwar jihar ta hanyar abin da ya kira “tasiri marar kyau”.

Shugaban kasa Trump ya ce zai dakatar da shigowar masu neman zama a Amurka daga ƙasashe masu tasowa, da suka shafi Afrika, Asia da Latin Amurka.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com